Rufaffen Sirri Hausa Novel Complete
*RUFAFFEN SIRRI*
*NA SADNAF*
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BISMILLAHI RAHAMANIR RAHEEM*
*PAGE 1*
“Ba abinda na tsana sama da abinda zai Shiga tsakanina da baccina,kamar na kurma ihun bakin ciki haka nake ji a lokacin da naji Abban Nusrah na ta shafani wanda nasan mai hakan ke nufi,tun kafin nayi bacci bai neme ni ba sai yanzu,ban motsa ba dan har ga Allah bazai samu abinda ya keso har ya gamsu ba,sai dai shi kadai yayi kidan sa yayi rawar sa duk da ba abinda ya shafe shi ko baccin nake idan yayi ra’ayi ko ban bashi hadin kai ba zai juyo dani ne ya samu biyan bukatarsa.
Ina Jin lokacin da ya rabani da zanin dana dora a saman t shirt din dake jikina,a madadin ya juyo dani sai naji ya rungumeni ta baya,ya fara k’ok’arin neman hanya da jikinsa dan tsawon zamana dashi ban wani san dan aike ba balle har wai a motsa min sha’awa,shi dai burin sa kawai ya shafani sama sama ya samawa kansa nutsuwa,inda naji Yana k’ok’arin yi yasa nayi saurin janye jikina,sai a lokacin na motsa na juyo Ina kallon sa cikin mamaki,shi kuwa idonsa a kankance ya kara jawoni,sai na juyo a rigingine dan ya samu abinda yake so dan Ina tunanin dan ta gefe yasa yayi hanyar da ba haka ba,sai dai a madadin ya hau kaina sai naga ya Kara juyar dani ya kankameni da hannu daya ya sa hannu daya ya Kara danna jikinsa wajen da yasa na Kara janye jikina da bala’in sauri na Mik’e zaune cikin mamaki Ina kallonsa.
K’ok’arin jawoni yake na janye jikina Ina “Lafiya kuwa Abban Nusrah mai haka”?
“Wane irin tambaya ne wanan Sajeeda bangane mai haka ba ki matso na samu nutsuwa ki koma baccin ki”
“To ai kai din ne bangane ba Kai ma kasan ba wajen nutsuwar ka nufa ba bayana naji kana k’ok’arin shiga”
Tsaki yayi ya Kara jawoni da k’arfi Yana “Ta bayan yafi dadi bari kigani”
Da karfi naga Yana Neman tura jikinsa bayana
Da k’ok’awa na fusge jikina cikin tashin hankali da mamaki na sauka daga gadon na nufi wajen haske na kunna na zuba masa ido kamar yanda shi ma ya zubo min ido, tamkar an like min baki haka naji dan tsabar mamaki na ma kasa magana,shekarar mu Ashirin da biyu da Aure bana Jin da gani har shi bakine a wanan fagen balle ince sani ne bai yi ba shi yasa yake k’ok’arin nema na ta baya har Yana cevmin yafi Dadi.
“Abban Nusrah anya a hayyacin ka kake kuwa”?
Mik’ewa yayi ya nufo wajen da nake tsaye yayi kasa da muryarsa yana “Sajeeda a hayyacina nake nasan zaki ji wani iri amma ki taimaka ki ba ni hadin kai ina so na gwada ta bayan nan ance yafi dadi”
“Allah ya kiyaye Kabiru Allah ya kiyaye ni zaka nema ta baya ta Inda ake kashi,kabiru Anya Kaine kuwa?waye yace ma ka nemi matar ka ta baya, idan Wanda ya baka shawara bashi da ilimi kai ina ka Kai naka ilimin bayan kasan haramun ne, bazan iya ba Kai ma da ka yi tunanin kayi gwajin ka fara istigifari”
Kasa ya Kara yi da murya cikin rarrashi ya matsoni Yana “Sajeeda yanzu baza ki iya taimaka min ba ki bari nayi sau d’aya sai muyi istigifari an dade ana kwadai ta min ta bayan nan haba matata”
Ya fara k’ok’arin rungumoni na ture shi da iya karfina dan zuwa yanzu ma sai naji tsoron uban yayana ya kamani,gani nake kamar bashi ba
“Kabiru Ina ga ba’a hayyacin ka kake ba a tsawon lokacin da nake tare da Kai nasan baka shaye shaye ballantana nace ba’a hayyacin ka kake ba,a iya sani na ka na da ilimin ka daidai gwargwado ka san abinda ya ke daidai da wanda yake haramun, bazan tab’a maka biyayya na Sabawa Mahallicina ba Ina mai rokon ka idan a hayyacinka ka ke wani ne ya baka shawara ka zo ka neme ni ta baya,ka gaggauta rabuwa da koma waye dan so ya ke ya Kai ka halaka”
Daga haka na nufi Kan gado na na dauki zanina na daura nayi hanyar fita daga d’akin ya hau kwalla min kira Yana
“Sajeeda Sajeeda karki sake ki bar d’akin Nan
Ko juyawa ban yi ba har na bar d’akin har lokacin ban daina mamakin sa ba.
Koda na fito dan karamin palon namu fitila na kunna idona ya sauka akan agogo naga karfe uku na dare na zauna akan kujera tare da dafe kaina jikina har rawa yake bansan tunanin ma da ya Kamata nayi ba.
Na kasa yarda da abinda ya faru yanzu a daki,na kasa yarda mijina uban yayana da shekarar mu Ashirin da biyu da aure da arzikin Yara biyar har mun aurar da Yar mu ta fari Nusrah shi ne yau dare daya zai nemeni ta baya wai ya dade yana san yayi gwaji an ce Masa yafi dadi har waye zai ce wa Kabiru ya gwada abinda Allah ya haramta.
Maciji ne shi Hausa Novel Complete
Sosai na zurfafa a tunani bansan tsawon lokacin da na d’auka Ina saka da warwara ba,sai Kiran sallah ne ya katse min tunanin da na tafi.
Mik’ewa nayi na koma d’akin.
A kwance na ganshi Yana dan girgiza kafarsa da alama ba Bacci yake ba idonsa biyu.
Bandaki na shige na daura alwala na fito har lokacin Yana kwance bai motsa ba,nasan fushi yayi,da ace wani abin na Masa da har zai yi fushi dani da sai na bashi hakuri,amma ni nasan ba laifin da na masa bazan tab’a masa biyayya a sabon Allah ba ba muyi haka tun kuruciya ba sai yanzu da muka Manyan ta,tsawon zamana dashi ban tab’a hana shi hakkin sa ba Koda kuwa fada mu ke amma dai yau na bijire masa dan bazan iya Sabawa Allah ba,
tsigar jikina har tashi yake idan Ina hararo yanda wai zai sadu dani ta baya.
Sallah nake amma na kasa yin sa a nutse sabida tunanin da ya dankare min zuciya.
Har na sallame Yana kwance zuwa yanzu sai naji kamar canzo kabiru aka yi bashi bane dan iya sani na baya Wasa da Sallah fushi dani bazai saka wai yak’i fita massallaci sallah ba.
Kasa hakuri nayi da carbina a hannu na Mik’e na zagaya ta wajen da ya kwanta Ina “Abban Nusrah “Abban Nusrah yau ba zaka yi sallah bane”?
“Dama can ke kike saka ni nayi Sallah”?
“Bani nake saka ka kayi sallah ba amma dai bai dace idon ka biyu kana Jin ana sallah ka k’i tashi kayi akan lokaci ba”
Tsaki yayi ya juya min baya.
Zuwa yanzu bazan iya fadan kalar mamakin da nake na sauyawar halin mijina dare daya ba,ga nemana ta baya ga k’in sallah.
Bai tashi ba sai da gari yayi haske ya shige bandaki ya dauro alwala yazo ya tada sallah Yana sallamewa ya fice daga d’akin.
A ranar sukuku na wuni na rasa mai ke damuna dan tunda Abban Nusrah ya fice daga gidan bai Kara dawowa ba.
Har karfe hud’u na yamma Ina zaune zuciyata fal da tunanin muryar Yasmeen ya katse min tunanin da na tafi “Umma ko dai magani zan d’auko miki ki sha”?
Girgiza kaina nayi na aro murmushi na yafa a fuskata sam bana so ta fahimci Ina cikin damuwa,dan nasan sai ta fini ma shiga cikin damuwar, kallonta da nake fuskar kanwata nake gani a fuskarta Margayiya Nuratu damuwar da nake ciki yasa naji hawaye na zubo min.
“Umma kuka kike”?
Share hawayena nayi Ina “ba kuka nake ba Yesmeen na tuna kanwata ne kawai Allah ya gafartawa Nuratu”
“Bata amsa ba illa idon ta da naga ya ciko da kwalla shekara goma kenan da rasuwar kanwata da ta kasance mahaifiyar Yesmeen.
Ruk’onta ya dawo hannuna Ina balain kaunar yesmeen tamkar yanda nake kaunar yayan cikina,
Yesmeen ta Kara siye zuciyata ne daga lokacin da rukon ta ya dawo hannuna,tana da bala’in biyayya da hankali duk wani abu data san ina so bata Wasa dashi bata da burin daya wuce taga ta faranta min ko Yaya ta gani a cikin damuwa itama tayi ta damuwa kenan.
Ko yanzu ma nasan ba lailai taci abinci ba sabida ta gani a cikin damuwa.
“Jeki d’auko mana abinci mu ci dan nasan baki ci abinci ba.
Tura abincin kawai nake ba wai dan Ina gane dandanon sa ba,na daure na hadiye damuwar da nake ciki dan Kar na Kara dagawa Yesmeen hankali.
Koda muka gama cin abincin daki na shige na cewa Yesmeen zan dan kwanta dan itace take yin aikace aikacen gidan Kamar yanda ta Saba kafin Nusrah tayi Aure tare suke aikace aikacen gidan,dan su biyu ne kawai Mata kannen Nusrah duka maza ne,Saifullahi Fahad Hamza da Annur.
Sosai na tsinci kaina a cikin damuwa dan tunda nake da Abban Nusrah bai tab’a fita Yana fushi dani ba dan muna samun sabani zamu shirya,duk da Yana da zuciya nasan hanyar da nake bi na shawo kansa,amma jiya abinda ya b’ullo min dashi ya girmama tunanina bazan tab’a iya barin sa ya neme ni ta baya ba sai kace wasu jahilai.
Karfe goma Sha daya ya shigo gidan fuskarsa a bala’in hade ina zaune a palo Ina jiran dawowar sa dan har yara duk sun yi Bacci.
Ko sallama bai yi ba ballantana ya kalli Inda nake, d’aki ya shige batare da ya amsa sannu da zuwan da nake masa ba.
Da ido na bi bayan sa Ina Kara mamakin fushin da ya ke dani na rashin gaskiya har ga Allah mamaki da al ajabi nake ,mik’ewa nayi na d’auko farantin da na jera abincinsa na bi shi d’akin.
Ko da na shiga a gefen gado na gan sa a zaune yana duba wani abu kamar a takarda ban dai san mai yake dubawa ba”
Na ajiye farantin a gefen teburin dake gefen gadon Ina
“Abban Nusrah Sannu da dawowa”
Bai dago ba ya cigaba da duba takardar Hannun sa
“Abban Nusrah mai na maka kake fushi dani?a iya sanina ba abinda na maka Abban Nusrah wani bak’on al amari ka zo min dashi wanda ni nasan kasan haramun ne,dagani har Kai ba yara bane,ga ta hanyar da Allah ya hallata ma ka neme ni ka samu nutsuwa dani,amma dare daya Abban Nusrah kace zaka neme ni ta baya ta Inda Allah ya haramta kaga dan na k’i bin umarnin ka bai Kamata kayi fushi dani ba dan babu biyayya a sabawa Allah,bansan waye ya baka wanan gurguwar shawarar ba,iya sanina duk wayanda kake mu’ammalla dasu ba mutanen banza bane bansan waye ya ce ma ka gwada ta baya zaka ji dadi ba,taya wajen da ake kashi yayi dadi Ni dai kayi hakuri zan iya k’ok’arina dan na gamsar da Kai amma ban da ta baya”
Sai a lokacin ya dago ya kalleni ya ajiye takarda a gefen pillo Yana “Sajeeda duk abinda nake yi Ina sane tsawon zamana dake Ina ga baki tab’a ganin na neme ki ta baya ba,gwaji ne kawai nake so nayi naji abinda ake ji ba wani abu ba,amma tunda kin nuna bakya so shikenan ba zan Kara nema ba,na dauka duk abinda nake so matsawar bai fi karfin ki ba Zaki iya min”
“Wanan yafi karfina ne Kabiru shi yasa bazan iya ba abinda akace haramun ne ban ga dalilin da zai saka kace zaka gwada ba mu fa ba Yara bane idan muna raye ma wani shekara zaka gan mu da jika”
“Ya isa haka Sajeeda Kinga na Kara neman naki ne yanzu”!?
Shiru nayi Ina kallon sa yaja siririn tsaki ya kwanta ya juya min baya.
Nace masa ga abincin sa yace bazai ci ba.
Wasa Wasa mijina ya fara fushi dani dan naki bari ya nemeni ta baya Wanda zuwa yanzu lamarin nasa ya fara bani tsoro ko Yaya na shawo kansa asan na faranta Masa rai, a madadin yayi ta hanya da ya dace sai naga Yana neman tura jikinsa bayana.
Halin nan daya bijiro min dashi ya matukar daga min hankali dan kullum cikin fada mu ke.
Gashi mu ba Yara ba ballantana nace wani Zan nemi shawarar sa Wanda ni nasan mu ya Kamata ma mu ringa hana wasu ba dai mu ba.
Ko a yanzu da ido nake bin sa har ya gama shiryawa bai ce min komai ba ya fice daga dakin na sauke ajiyar zuciya ina tunanin mafita Kiran Nusrah daya shigo wayata ya katse min tunanin da nake.
Ina dagawa muka gaisa kamar yanda muka saba Inda take sanar min zuwan ta anjima na ajiye mata dambu na saki murmushi Ina sai ta zo.
Na Mik’e nayi waje dan na fadawa Yesmeen zuwan Nusrah duk da nasan kila ma sun yi waya.
Ina fitowa naga Abban Nusrah a zaune a doguwar kujera duk a tunanina Yama fita ashe fitowa yayi ya zauna a palon.
Yesmeen kuma na tsugunne a gabansa tana hada mi shi shayi.
Fitowa ta yasa ta dago tana “Umma Ina kwana”
Zama nayi a gefen shi fuskata d’auke da faraa na hau amsa gaisuwar ta ko kad’an bana so yarana su fahimci wani abu.
Tana gama hada masa ta mike tana bari ta d’auko kofi ta hado min shayin na girgiza mata kai akan ta bar shi sai anjima.
KABIR
Da ido ya bi Yesmeen din har ta shige d’aki ya d’auki shayin ya fara kurba a hankali har ya shanye Yana Jin idon Sajeeda a kansa.
Yana dire kofin ya mik’e yayi waje batare da ya tsaya Jin mai Sajeeda ke cewa ba.
Yana fita ya haye machine din sa bai zame ko’ina ba sai wani hadadden gida da fadar haduwar sa bata Baki ne.
Mai gadi ya riga da ya gane shi hakane yasa ya bude masa ya shige da machine dinsa kansa tsaye ya nufi d’akin saukar baki dake farfajiyar gidan.
Kamar yanda yayi tsamani a zaune ya tarar da Alhaji Rabiu a cikin dakakiyar shaddarsa dake ta kyalli kamar madubi.
Sai da Kabiru ya sama wa kansa wajen zama.
Alhaji Rabiu yace “An dace kuwa”?
Sai da Kabiru ya sauke ajiyar zuciya yace “wlh ba’a dace ba duk ta inda kake tunanin zan biyo mata na biyo mata wlh tak’i bani hadin kai”
Murmushi Alhaji Rabiu ya saki Yana “Na fa san irin su haka suke da balain taurin kai Amma idan tasan wata ai bata San wata ba ka tashi muje wajen shugaba mu masa bayani”
Ya mik’e Yana k’ok’arin yin hanyar waje.
Kabiru yayi saurin dakatar dashi yana “Rabiu Ina kaunar matata tunda na yarda zan yi harkar nan zuciyata take cike da fargaba da tsoro ko bacci bana iya yi dan Allah muje wajen shugaba ka fada masa ya duba min ko zan iya yi da wata na samu biyan bukatata ba sai Sajeeda ba.
“Ikon Allah toh wa zaka samo”?
“Akwai yar kanwarta da nake rike da ita da ita nake so na samu biyan bukatar tawa”
“Bani da ta cewa muje daga can muji ko zai yu……
Hmmm
*RUFAFFEN SIRRI*
*NA SADNAF*
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*Page 2*
Kabiru har suka je Suka dawo bai iya magana ba sabida kasan zuciyarsa cike take da tsoro,ji yake Kamar ba zai iya ba dokokin da Abubuwan da akace yayi sun masa yawa da tsauri,a hankali ya Kai dubansa wajen Alhaji Rabiu da ya kasance abokinsa tun primary da a lokacin ya fi shi k’ok’ari nesa ba kusa ba dan shi yake zuwa na karshe ma a ajinsu da kuwa suka gama primary bai Kara saka shi a idonsa ba,bai Kara jin labarin sa ba sai a shekara biyu da suka wuce ya had’u dashi,sai da yayi da gaske ya gane shi sabida yanda ya dawo fari kal sabida yadda hutu da Jin dadi suka zauna masa tashin farko,kyautar dubu dari ya Masa,ya hada da bashi lambarsa,duk kalar rayuwar da yaso tun Yana karami na rayuwar Jin dadi shi yake gani a wajen Rabiu.
Gashi ya girma zai iya cewa ya d’auko tsufa tunda Yana dab da aurar da ‘yar cikin sa duk bai samu cikar burin nasa ba.
Tuni yaji ya kwadaitu da san yayi kudin fiye ma da da hakane yasa ya makalewa Alhaji Rabiu ko zai taimaka Masa ya sama mi shi aiki irin nashi da shi ma zai samu kudin.
A haka Alhaji Rabiu ya ringa masa yawo da hankali Yana kasuwanci yake yi sai da yayi dagaske Rabiu ya fito ya nuna masa ta hanyar da ya samu kudin sa,idan har yaga zai iya.
Tsayuwar motar Alhaji Rabiu a wani tamfatsatsen gidansa da matarsa ta uku take ciki ya katse tunanin da Kabiru ya tafi.
Yayi horn Mai gadi ya bud’e masa.
Tun da suka shiga gidan Kabiru ya saki baki da hanci Yana kallon Aljannar duniya,maganar shugaba na dawo Masa a kunne,”zaka yi kudi, idan nace ma kudi,Ina nufin kazamin kudin da zai saka duniya ta san ka zaka ji dadin rayuwar ka zaka bar wa yayanka tarin dukiya ka tabbata baka tsallake duk sharuddan da aka gindaya ma ba daga yanzu kafin wata ukun zaka fara dandana arziki amma ka iya takun ka”
“Sauko mu Shiga daga ciki ka gaisa da Aseeya”
Muryar Alhaji Rabiu ya katse Masa tunanin da yake.
“Rabiu anya zan iya wlh bansan mai yasa nake Jin bazan iya ba gani nake za’a iya gano ni da wuri bazan iya yiwa Sajeeda haka ba”
Murmushi Alhaji Rabiu ya saki Yana “Tunda na iya yiwa Sakeena Yar uwata haka Kai ma zaka iya bafa kasheta zaka yi ba,a cikin kankanin lokaci Kai ma zaka zama kamar ni,kayi amfani da abinda kake dashi ka samu cikar burin ka,kar ka karaya abokina muje dai daga ciki indai Muka bi komai a yanda Muka tsara wlh baza’a samu matsala ba”
Kabiru gyada Kai yayi duk da a kasan zuciyarsa gani yake bazai iya ba.
Yabi bayan Alhaji Rabiu yana karewa gidan kallo,hararo kansa kawai yake a matsayin Rabiun ya mallaki irin wanan gidan,ya ginawa su Saifullahi manya manyan gida daidai da Nusrah ma sai ya mallaka Mata gida da mota, tuni yaji ya Kara kwadaituwa da ya samu kudin,a lokacin da suka Shiga palon da Kamar a kasar waje suke da suka shiga.
A lokacin kuwa daya zauna kalle kalle ya cigaba da yi Alhaji Rabiu ya haye Sama minti biyar a tsakani sai gashi ya sauko ya zauna.
Kafin kace me masu aiki sun cika gabansu da kayan ciye ciye.
Alhaji Rabiu kuwa sai murmushi yake dayaga yanda Kabiru ke hadiyar yawu.
Takun takalmin Aseeya matar Alhaji Rabiu dake saukowa daga saman benen yasa Kabiru maida hankalin sa wajen benen.
Yarinya ce bata fi saar Nusrah Yar sa ba ko zata girmi Nusrah bazai fi da shekara biyu ba,kyakyawa ce ta ajin karshe tamkar ita tayi kanta fuskarta d’auke da murmushi,har ta karaso gefen Alhaji Rabiu ta zauna ta fara gaida Kabiru da ya hau washe baki kasan ransa Yana ta mamakin yanda yarinya karama ta yarda ta auri sa’an mahaifinta.
Bayan sun gama gaisawa ta mik’e ta koma sama,
“Rabiu yanzu Wanan Yar yarinyar ka Aura”?
Murmushi Alhaji Rabiu ya saki ya zuba Lemo a kofi sai da ya kurba ya ajiye ya kalli Kabiru Yana “Shekara uku kenan da Auren mu Kuma ta wajen nan da matarka ta hana ka ta wajen nake neman ta”
Ido Kabiru ya zaro waje Yana “Kuma sai ta yarda”?
“Kwarai kuwa ba Ina da kudi ba,a yanzu da kake ganin ta bama tasan Inda zata Kai kudi ba kaga kuwa ko dan su dole ta yarda da bukatata dan sai da na tabbata Iyayenta irin talakawan nan ne sosai,dan a garin talla ma na hadu da ita,na cikata da kudi na cika Iyayenta da kudi, basu da gidan kansu kafin na aureta yanzu kuwa har yayyenta maza ba Wanda ban siyawa gida ba tana morata a zahiri Ina morarta a badini”
Sai yayi kasa da murya
“Tana samun ciki take b’ari na riga na bada mahaifarta”
Ni kuwa Ina nan da yayana bakwai suna jin dadin su a waje”
Kabiru mamaki ya sa ya kasa ma magana dan sai a yanzu ya gane da rabon amaryar kudin sa ke Kara hab’aka uwar yayan sa kuma ta masa silar kudin.
“Rabiu dama nima na auri wata ta zama silar kudin bana so na tab’a uwar Yayana da mu ka Sha wahala tare da ya Kamata ace a yanzu taji dadina shugaba ya bani wata uku ya bani Abubuwan da zanyi har zuwa matakin karshe,tunda Muka baro wajensa wlh jikina a sanyaye yake gani nake bazan iya ba”
Wani irin mugun kallo Rabiu yabi Kabiru da shi yana “Ka ga idan baza ka iya ba ka tashi ka bar min gida ka Kuma dawomin da kudadena da na baka,kudin nan idan kayi ni zaka bawa ko me ana ta nuna ma hanyar arziki kana baudewa,duk uban wahalar nan da ka ringa bani dama baka tsayar da zuciyar ka ba abu kad’an sai kace baza ka iya ba dalla tashi ka bar min gida kasan Kuma baa yiwa kungiya haka indai ka fasa wlh sai an tab’a ka”
“Ba abinda nake nufi ba kenan Rabiu ba fasawa zanyi ba sharrudan yanzu sunfi bani tsoro ina tsoron na kuskure a samu matsala”
“Ka kwantar da hankalin ka kasa a ran ka zaka iya Sajeeda da kake ta fadi ba fa kasheta zaka yi ba balle,dadin ma da ita za’aji gefe guda Kuma idan an kwana biyu zaka iya auren Mata uku kayi ta more rayuwar ka abokina kana Jin dadi,yayanka ka gan su fes,ni kasan gabad’aya yarana suna kasar waje,shawara daya dai Zan baka duk yanda muka tsara ka bi zaka Sha mamaki kila.ma.ka fini himma wajen bada abin arziki kudi suyi ta hauhauwa ai ba dawwama zamu yi muna yi ba zamu Yi iya yin mu kudin ya Kai mana yadda muke so sai mu tuba muyi ta istigifari Allah Mai yawan afuwa da gafara ne zai yafe mana duk shekara muna d’akin sa muna neman yafiya fa wanan ba wani abu bane”
“Hmmmm toh shikenan Allah yasa duk Kar na samu matsala Ina Addu’a Allah yasa Kar Sajeeda ta tab’a rafkoni dan tana da balain wayo da san tabi kwakwafi”
Da haka suka cigaba da hirarsu wajen laasar Alhaji Rabiu ya Kara tsara masa duk yanda za’a yi ya d’auko kudi ya bashi mai yawa ya raka shi ya tafi.
Sajeeda
Idan naga yarana gabad’aya a gabana ji nake kamar banida wani matsala a rayuwata, zuwan Nusrah yasa na manta da damuwa da hawan jinin da Abban Nusrah ke neman saka min,Ina zaune a tsakiyar su duk mun baje a tabarma ana ta hira, wayarta ya hau ringing tak’i d’auka ganin Kiran ya Kara shigowa nace “Wai ba za ki dauki wayar ki ba ko ba kiran ki ake ba”?
“Umma Ahmad ne fa na san cewa zai yi na dawo ni Kuma na fi so na gaisa da Abba kafin na tafi na ga kowa ban dashi bazan ji dadi ba idan ban gan shi ba”
“Sai ki Kira shi a waya ku gaisa maza tashi ki tafi gidan ki bana San shashanci dama mijin ki ke ta Kira kika k’i d’auka”?
“Umma dan Allah ki bari na Kira Ahmad nasan bazai hana ni jiran Abba ba”
Sai da na ga ta kira mijin ta ya amince ta jira Abban ta kafin na yarda ta zauna duk da har a kasan raina ba gajiya nayi da ganin ta ba gani nake kamar jiya na haifeta sai gashi cikin ikon Allah da ran mu ta girma tayi, aure duk Wanda ya ganta yasan tana d’auke da karamin ciki,a tunanin da nake na tuna halin da mahaifinta ya bijiromin dashi,take da girmana da komai nabi sauran kannenta da kallo da duk sun ma fi Nusrah girma Annur da Fahad ne kawai basu fita girma ba,mutane da yawa sun d’auka saifullahi yayanta ne da yake girman yazo da zamani har wani saje da gemu ya ajiye, ba Mai yarda ta girme shi,
Shigowar Larai da sallama yasa Mu ka mai da hankalin mu wajen k’ofar tare da amsa sallamar da tayi,Larai yar aiki ce a wani gida dake bayan layin mu na riga da nasan da zuwan ta tunda hajiyar ta kirani akan zata turo ta ta kawo min kayan aiki.
Buhun hannun ta ta fara ajiyewa kafin ta sauke kayan dake Kan Almajirin dake biye da ita a baya ta zauna muka gaisa
Tana “ga kayan nan Hajiya tace ki duba abinda babu sai na karbo”
Kayan na duba naga duk abinda na bada list Ina bukata akwai hakane yasa na dago Ina “Karfe uku ne taron ko?
“I karfe uku ne idan Allah ya kaimu”
“Toh ba damuwa gobe karfe daya da rabi kizo da kulolin zuwa lokacin na gama in sha Allah”
Mik’ewa tayi ta min sallama ta tafi,
“Umma dan Allah ki daina wanan aikin wahalar wlh har ga Allah bana so sabida ke nake so na nemi kudi ki huta”
Cewar Faisal yana hade rai.
Saifullahi ya karba da “Abin nan na cimin tuwo a kwarya wlh nima bana san aikatau dinan da take karba kudin ma ba wani Mai yawa ba a gaskiya lokaci yayi da Zaki daina wanan aikin umma”
Murmushi na saki Ina “Ina ga tunda kuka taso kuka same ni da sana’ar nan, ni kadai nasan kalar rufin asirin da wanan sana’ar yamin bani kadai ba har daku tunda kunsan aikin baban naku ba wani mai kwari bane idan na daina ku kan ku zaku Sha wahala a yanzu idan ta biyani kudi na gobe shine zan samu kudin registration din jamb din ka”
Yana k’ok’arin magana Abban Nusrah ya shigo da sallama hannun sa d’auke da ledoji niki niki.
Tuni yaran Suka mimike Nusrah ta riga su isa wajen sa tana “Abba oyoyo tun dazu nake jiran dawowar ka sannu da zuwa”
Washe baki yayi Yana “Kin dade da zuwane”
“Kana fita nazo Abba”
“Ai da kin kirani a waya ai da na dawo da wuri ya kike ya maigidan naki”
A kunyace Nusrah ta ringa amsawa Bayan ta ajiye ledojin.
Daya bayan daya suka ringa Masa sannu da zuwa fuska a washe ya ringa amsawa sai da ya juyo muka hada ido ban kawo zai min kallon arziki ba naga ya sakar min murmushi take na saki murmushi Ina Jin dadi a raina na Masa sannu da zuwa a daidai lokacin da Yesmeen ta d’auko masa ruwa ta ajiye a gabansa.
Ganin su Saifullahi na k’ok’arin mik’ewa yasa yayi saurin dakatar dasu sai da suka zauna ya kalli Saifullahi Yana “Ni nawane ma kudin registration din ka”
Washe baki Saifullahi yayi Yana “Abba na dan yi aikin lebura na tara dubu goma yanzu ciko nake nema”
“Nawane cikon”
“Dubu goma Sha biyar ne”
Hannu yasa a Aljihu ya d’auko wrapper Dari biyar biyar,na gwallo Ido Ina kallon sa tamkar yanda duka yaran suma suka zaro ido suna kallon kudin,ya kirgo Dubu ashirin dan dani aka kirga kudin ya mikawa Saifullahi Yana “gashi nan kaje kayi registration din”
“Na gode Abba Allah ya Kara arziki”
“Ameen”
Ya kalli Faisal yana “nawane kudin jamb din naka”
Shima baki a washe ya fada masa ya kirga ya bashi zuwa lokacin farinciki da mamakin Inda ya samu kudi Mai yawa hakane ya cikani dan iya sanina yanzu ba lokacin samun kudin sa bane
Dan aikin nasa sai lokacin zafi sosai idan ya samu su gyaran freezer haka Ac franker da sauran su.
Mamaki bai Kara kasheni ba sai da naga daidai da Annur sai da ya tambaye shi matsalarsa ya kirgo kudi ya bashi ko Nusrah bai bari a baya ba ya kirgo Dubu goma ya bata har ga Allah kasa motsi nayi dan a lissafin da nayi ya bada wajen dubu sabain,Ina ya samu irin wanan kudin mai yawa haka yadda ya bawa Nusrah dubu goma haka ya bawa Yesmeen da bakin su ke washe suna ta zuba Mai godiya da Addu’a sai amsawa yake bakin sa shi ma a washe.
Sai a lokacin yacewa Yesmeen ta d’auki ledar kajine a ciki ta wanke ta dora sai yarana suka Kara haukacewa da murna har Nusrah na wlh sai ta tsaya an gama ta tafi dashi.
Sai da duk Suka watse ya juyo ya kalleni yana “Hajajju yau nima na dan yi abin kwarai rabon da na yiwa yaran nan abu da kaina har na manta baki ji dadin da naji dana ga farin ciki a fuskarsu ba”
Murmushi na saki Ina “Allah ya Kara arziki ya Kara budi ni da adashe na ma Zan dauka na bawa Saifullahi yayi registration din sai Kuma Allah yayi ikon sa ka samu kudi”
“I Allah kuwa yayi Ikon sa Alhamdulillah ke ma ai ga naki siyayyan nan na miki”
Ya turo min daya ledar gabana
Baki a sake na bud’e ledar naga less ne guda biyu sai atamfa da wani bakin mayafi duk da ba wani sanin kaya masu tsada nayi da gani kayan masu tsada ne”
“Abban Nusrah a Ina ka samu kudi mai uban yawa haka”
Kabiru gyada kansa yayi dan yasan zaa rina indai Sajeedar daya sani ne sai ta tambaya
“Haduwa nayi da wani tsohon abokina ya zama mugun mai kudi,shi yamin kyautar kudin nan bai tsaya iya nan ba yace zai taimaka min na samu aiki”
“Wane abokin naka ne dan Kamar duk nasan abokanan ka”?
“Aa baki san wanan ba primary Mu ka yi tare”
“Allah sarki Allah ya saka Masa da alheri ya biya Masa bukatunsa na alheri yadda ya faranta mana Allah ya faranta masa”
“Ameen ya Allah”
A ranar tare duk Muka ci abinci cikin tsananin farin ciki su Annur a kudin da aka basu har da siyo sababin takalma.
Abban Nusrah ma zan iya cewa rabon da naga farin ciki haka a fuskarsa har na manta.
Bayan sallah isha mijin Nusrah yazo Suka tafi.
Addua kawai nake a raina Allah yasa Abban Nusrah ya cire wanan mumunan abin a zuciyar sa har ga Allah naji dadi da naga baya fushi dani bana san abinda zai Kara sawa na mu yi fada.
Ko da muka kwanta a ranar bai neme ni ta baya ba ta hanyar da Allah ya hallasta miji ya nemi matar sa ya neme ni bayan ya samu nutsuwa ya bani hakuri akan na kwantar da hankalina bazai Kara tunanin nemana ta baya ba sai a yanzu ma ya ringa nadama da yayi tunanin gwadawa.
Har ga Allah naji Dadi rumgume da juna muka yi Bacci.
3am
Kabiru a hankali ya leka fuskar Sajeeda yaga tayi nisa a bacci.
Ya zare jikinsa daga nata ya sauko a hankali sabida Kar ya tasheta daga bacci.
Gefen gadon ya duba a hankali ya d’auko pant din ta ya kudundune a hannun sa cikin sanda ya fice daga d’akin yayi waje.
Yana zuwa yayi bayan gida ya d’auko tukunyar kasar da ya shigo dashi da ba Wanda yasan ya shigo dashi,ya saka pant din a ciki ya fara surutan da aka ce yayi a hankali Yana waige waige duk da Yana da tabbacin ba Mai ganin sa dan a sharrudan ance Kar ya sake ya yarda a gan shi.
Yesmeen.
Bata da nauyin bacci ko kad’an ko ya taji motsi sai ta farka.
Motsin k’ofa yasa ta bude idonta.
Kafin taji Kamar takun tafiya a ta Bayan dakinta Inda ta mik’e zaune tare da dafe kirjinta cike da tsoro.
A hankali ta Mike ta leka ta window……….
MG’S SKINCARE
Dame akafiki yar uwata?
Kyan fatar ko iya gyaran fatar?
Ina riba g macenda t Maida kanta sauran mata?
Shin haryenzu labarinmu kikeji ko kike bayarwa?
Hajiyata miye matsalar?
Fatar takice abun se lahaula?
Kingwada kingwada harkinsare?
Tsakanida Allah yaushe daren yayi balle wayewar garin?
Inbakida labarin MG’S wacce tasanki tasansu,
Gawurtaccen Kuma shahararren kamfanin gyaran fatane,duk lalacewar jiki,duk hautsinewar fata,duk yenda jikinki yazama abun kunya gareki, Ina tallata maki me gabadaya,
Muntarkato,munwarwaro,munqullo duk wani Abu daze maidaki wanke hannu kataba mun qara a cikin kayayyakinmu,muncire,muntsife,munfidda,mun tantance mun hadamaku wasu irin hadaddun lafiyayyun kaya masu masifar goge fata,wallahi duk fitinar fatarki inshallah,kinzo bustop,kisiya kiyikyanda ko mace,kan juyo ta waiwayo ta dubi halittar Allah,
Ga product din kamar hka,
Sabulu 4k
Mg’s beauty kit 14k
Herbal whitening soap
Body cream
Face cream
Scrub
Cleanser
Glow oil
Sannan akwai flawless skin beauty kit 16k
Tsakanida Allah kigafa
Duk wannan garabasar Kuma kinazaune hba taso a dama dake a harkar yar uwata,
Ayi hakuri da sauyin farashi komi yatashine muma b hka mukasoba
Chat:08062991549,07046881166,07067210195,
Call,+2348064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg’s skincare
Team glow😍
[…] Rufaffen Sirri Hausa Novel Complete […]
Masha Allah inason complete dinshi pls