Ni da Yaya Arman Hausa Novel Complete
NI DA YAYA ARMAN
Hot love story
“`MALLAKAR“`
*Hajara L Sadeq*
~Marubuciyar~
Komai mukaddari ne
K’addarar soyayya ta
Najmat Abiy
And now
*NI DA YAYA ARMAN*
*JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION*
*GODIYA* godiya ta tabbata ga Allah (S W T) tsira da Amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad(S A W) da ahalinsa da sahabbansa ina Godiya Ga Allah (SWT) da ya k’ara bani ikon fara rubuta littafin nan yanda na farashi lafiya ya sa na gama lafiya cikin yarda da amincewarshi.
*GARGAD’i* ban yarda wata ko wani ba su juyamun Littafi ta kowace sigaba muddin Hakan ta faru zan d’auki mummunan mataki.
Dafin Namiji Hausa Novel Complete
Littafin nan NI DA YAYA ARMAN k’irk’irarren Labari ne Idan yazo daidai ko yayi shige da labarinki kiyi hakuri arashi ne.
*DEDICATED TO SISTER LEMART L SADEQ*
Y’ar uwa,Masoyiyata,Aminiya,Besty love Bazan tab’a iya misalta soyayyarki a cikin zuciyata ba Allah ya barmu tare my y’ar uwa Rabin jiki littafin nan gabaki d’ayanshi sadaukarwace gareki ki kiyi yanda kikeso dashi
23/May/2022
بسم الله الرحمن الر حىم
*BOOK ONE*
🅿️………1&2
“`Kano state“`
~Nasarawa Quaters~
Tsit kakejin unguwar tayi shiru kasancewar ranar da ake gallawa kowa ya na gidajensu Unguwace ta y’an gayu yawaicin masu kudi sunfi zama unguwar gidaje ne na alfarma Chan na Hango wani tafkeken gida mai matuk’ar kyau da tsaruwa da kuma girma na ban mamaki Dan gate din gidan kanshi zai d’auki sama da mota sha biyar gidan gida biyu ne na kusa dashi Shima yana da kyau daidai misali Shima da gate d’inshi amma kuma akwai kofa wacce daga cikin gidan zaka bulla d’ayan gidan ba tare da kasha wahalar zagayawa ba cikin gidan ya hadu komai cikin tsari.
Zaune take ta na guga ta na yi ta na Jan tsaki Inna dake zaune ta na taunar goro ta ce “da yake uban wani ya sanyaki gugar da zaki zauna tun d’azu kina yiwa mutane tsaki aikin b’urut inji tusa” Aira da a cike take daman cike da jaraba ta juyo ta ce “waike inna ina ruwanki dani ne,dandai neman tashin hankali irin naki magana nayi maki ne Dan ayi maki magana ki ce anyi maki Rashin kunya kije ki hada mutum da Abba ni kibarni da gajiya ta ma ta isheni”da ruwana dan ubanki shegiya mai kama da Aljannu figai figai kamar kaza amma sai Rashin arziki cike da ciki” tsaki taja tare da cire gugar ta mik’e tana hada kayan gugar ta ce .
“Kindai kusa mutuwa mu huta ” Inna cike da masifa ta dauki pillow dake kusa da ita ta jefa mata tace “uwarkice Rahama zata mutu Dan ubanki Da gudu Aira ta yi waje ta na Dariya Dan tasan yau ta tabo inna Dan ba abunda ta tsana irin kace za ta mutu.
Ta na fitowa ta na Dariya sai sannan na k’are mata kallo Fara ce Sol farin nata har wani yellow yellow yake doguwace daidai misali sannan bata da k’iba siririyace amma ba Chan ba Dan tsawonta ne ma yasa za akirata da siririya badan haka ba ta na da kibar ta daidai gwargwado,ta na da shape sosai Musamman Hips Dan koya tayi tafiya saisun juya zaka iya kiranta da mai shape din cocacola bata da breast sosai Amma kuma bazaka kirata da kwaila ba Ta na da y’ar doguwar fuska ta na da dogon hanci da kuma k’aramun bakinta da yayi das da kyakyawar fuskarta lips d’inta jawur kamar ta shafa janbaki sanye take cikin wasu English wears Riga da wando ba kallabi kanta bak’in gashinta ne tayi parking Wanda ya dirar mata har gadon baya kyakykyawace sosai ta Bugawa a jarida Saidai daga kaga fuskarta kasan yarinyace girman jikine kawai Allah ya bata amma bazata wuce 17 years ba.
Ta d’ayar kofar ta bi ta shiga cikin gidansu ta na shiga ta Hango Abba akan farar kujera sanye da glass yana karanta jarida kai tsaye wajenshi ta nufa ta na murmushi ta ce ” Abba Sannu da hutawa”Cikin muryar girma da dattako ya d’ago ya Kalleta da murmushi a fuskarsa ya ce “Yawwa y’ar gidan Inna ” sannan ya maida kanshi ga abunda yake hakan yasa ta tafi ta shiga cikin gida.saida na K’are mashi kallo naga kamarshi d’aya da ita sak kawai Haskene ta fishi.
Tana shiga palourn ta tarar da duk y’an gidansu suna zaune yaran na shirin tahfex iyayen kuma na zaune suna hira ta na shiga Mamy ta ce “gwara da Allah ya kawoki yanzu nake. Cewa Aje a kiraki Kuyi shirin Tahfex”Mamy Fara ce itama sosai kamar Aira Saidai basa kama sosai ita Aira ta d’auko farin mahaifiyarta ne Amma sak Kamar Abbanta ta yo.
Turo baki gaba ta yi ta ce Daman banzoba wlh ni na gaji Duka yaushe na dawo daga school bama wannnan ba sanin kanku Waec muke Ni nadauki hutun Tahfex d’innan gsky saimun gama jarabawa” Salati Mamy tayi tace “Aiko baki isa ba wlh ko ki tashi ki shirya ko yanzu nakira Abbanki na fad’a mashi” wara idanu tayi Dan a rayuwa ba Wanda take shakka irin Abba bayason wasa da Ilimi musamman Na Arabi hakan yasata jin Haushi kamar zatayi kuka Mama ce ta ce “Kiyi Sauri Kinga y’an uwanki harsun shirya ai ba a wasa da Ilimi a zamanin nan Daughter bare kuda har kunyi sauka hardace kuke had’ewa kinaga itama harkun tafi Hizif Arba’in ai kamar yaune zakiga kun hade” To Mama bari naje na saka kayan Amma Dan bazan koma ba na tab’o inna tafada ta na Dariya “Murmushi Mama ta yi ta ce ” Ai keda Inna ba a shiga Mamy ko tuni harta tashi ta shiga ciki.
Ta na shiga d’akin ta tarar da Su Amma harsun shirya ta ce “Sister Dan Allah aramun Kayanki insa”tana saka hijab ta ce ” ke ina taki “cikin masifa ta ce ” to ina ruwanki da ina tawa ko Dan nace ki aramun kayan ki shine zaki fad’amun magana “Amma ta ce” To Allah huci zuciyarki kidaga locker ki dauka kinci sa a An goge”Ummy dake gefe ta na chat taja tsaki ta ce “Kede Anyi sokuwa wlh idan nice Saidai ta mutu Amma bazan ba ta ba ta na kanwarki amma duk tabi ta rainaki” Tsaki Aira taja jin Abunda Ummy tace ta ce Ke ina ruwanki shigar shugula kawai ke har kin isa ki shiga tsakanina da Amma kidaina shiga sabgarmu dalla tafada ta na sanya kayan da ta dauko, dariya itama amma tayi ta ce”Ai shine ko ina ruwanta da shiga tsakaninmu” tabe baki ummy dan daman tasan ba a shiga tsakaninsu sanin ta biyewa Aira tsaf zatayi mata Rashin kunya ya sanya Ummy Jan bakinta tayi shiru ta ci gaba da chat d’inta.
Bayan sun dawo da daddare D’akin Inna ta shiga ta na shiga ta fara balbaleta Tayi banza ta kyaleta ganin abun ya fara yawa ya sanyata tashi ta shiga bedroom d’inta ta d’auko wasu manya-Manyan chocolate guda biyu ta kalli inna ta ce “indai kina so in baki to wlh sai kinbar fad’an nan” tuni inna ta fara washe baki ta ce “Ah too Y’ar lele na daman akwai Zumar turawan nan a gidan nan.”
” Dariya Aira tayi tare da mik’a mata tace “Ai fad’an ki yasa bana baki ” amsa inna tayi ta na washe baki ta daga ta fara sha har wani lumshe ido take Aira tayi kasa da murya tace “Ai Hajiya inna sai kinyi shekaru irin na Dabino keda mutuwa ta yi nan kinyi Chan Yanzu Dan Allah My Inna wayarki zaki aromun yanzu zan maido maki ” kai kede Allah yayi miki albarka yarinyar nan Duk a d’iyan Habubakar ke kika fita zakka duk kinfisu hali me kyau bakisan in mutu Sannan ta ciro wayar a d’an tofin ta ta ta mik’a mata ,itadai Aira Dariya kawai take jin yabon da inna ke mata kamar ba itace ta gama balbaleta ba tasan daman tunda ta bata choculate ta kashe bakin.
Itako tashi tayi ta shiga bedroom d’inta ta haye kan Gado tare da Rungume pillow jujjuya nokiar inna tayi tare da dialing number daman tana kanta tana kira taji a kashe ta sake kira yakai goma amma abunda ake cemata kenan kuka ta fashe dashi ta ce “Yaya ina ka shiga tun jiya wayarka kashe na shiga ukku Kardai wani Abu ya sameka, ta jima ta na kuka ta na sabbatu tana kiran number a kashe Dan tab’a saba da missing d’inshi daidai da yini daya ba hakan yasa ta k’ara shiga damuwa da kyal ta samu wajen 1 bacci ya dauketa.
Washegari sukuku ta tashi duk hankalinta ba kwance ba haka dai har taje school tayi jarabawa amma hankalinta ya na wani wajen daban.
©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️
*Government House*
Ko ban fad’a ba kunsadai yanda gov house yake ba sai na bata bakiba wajen fad’an tsaruwarta da kyanta ba duk yanda zan kwatanta kunsan tafi haka.
Yau duk gidan aikace aikace kawai ake da shirye shiryen Abinciccika kala kala Dan tarbar tilon d’an governor mai ci yanzu da zai dawo daga London Mahaifiyarshi Hajiya Fatima yau cikin farinciki take marar musaltuwa Dan sosai tayi missing d’an nata Da misalin k’arfe Shida ya yamma jirginsu ya Sauka a Nigeria Mahaifiyarshi da kanta suka tafi domin tarbarshi .
A hankali yake Saukowa daga matattakalar benen jirgi cikin Tafiyarshi ta k’asaita sanye yake cikin K’anan an kaya da sukayi mugun Karbarshi Fari ne amma ba wai fari Chan ba dogo mai murdaddan jiki yana da saje Wanda shine Babban abunda yake rikita y’an mata lips d’inshi ko har wani ja yake kamar ya shafa wani abu Kyakkyawa ne na Bugawa a jarida daga ganin fatarshi kasan Hutu ya zauna mutum ne Mai ji da gayu Shima kallo d’aya zakayi mashi kasan ya na cikin tsananin farinciki hug din juna sukayi shida mahaifiyarshi cike da son juna da kewar juna suka koma gida suna hirarsu ta y’a da uwa koda suka isa gida baiyi mamakin tarbar da ya samu ba Dan ko da kwana daya ne yayi tafiya haka ake mashi.
Bayan yayi wanka ya sake shiri ya huta mahaifiyarshi da kanta ta dinga feeding d’an nata kamar wani yaro shi kuma sai shagwaba yake mata kamar zaiyi kuka ya ce “Uhm mummy na k’oshi please ki barni haka cikina ya cike”mummy na k’ara d’auko wani spoon din ta ce ” Haba son Bafa kaci da yawa ba nasan a can ba wani cin abinci kake sosaiba ha a d’aga bakin saika cinye na plate d’innan”.
“Murmushi kawai yayi a haka dak’yal har ya ida cinyewa Dan shi ba mutum bane mai fiyason cin abinci ba ya na gamawa ya Mike tare da kallon Mummy ya ce Mummy zan d’an fita please karki hana” Haba son ko fa hutawa bakai ba daga dawowarka ka ce zaka fita “cikin shagwaba ya ce Mummy ba jimawa zanyiba yanzu zan dawo ” To bazaka bari sai ka kara huta wanna”Mummy please” yafada yana hade hannaye,To shikenan Allah ya kiyaye ka kulamun da kanka kuma karka jima”Hug d’inta yayi ya ce “Don’t mention my dear mom saina dawo.
Driver kadai ya tuk’ashi Dan bayason yawo da Security wannan Karin ma yayi kyau sai baza k’amshi yake Dan shigar da yayi ta yanzu ma tafi ta d’azu kyau murmushi kawai yake shi d’aya.
Aira suna zazzaune a palourn inna Ita da su Amma,Haidar sai Ummy duk suna shan labari wajen inna sai kwasar Dariya suke banda Aira da tayi jugum Dan yau ko abincin kirki bataci ba Suka jiyo knocking Haidar ne ya tashi ya je ya bud’e Aira da hankalinta na kan k’ofa ganin mai shigowarne ya sanyata mik’ewa a matuk’ar rud’e ba k’aramun surprise d’inta yayi ba shima tsaye yayi ya na K’are mata kallo sanye take cikin wasu English wears Riga da wando red and black kanta bako kallabi sai gashinta da yake a parke Sosai yaga ta k’ara yimashi kyau da girma A d’an kwanakin da yayi bai ganta ba murmushinshi kawai mai tsada yake sakar mata Ai bata San Lokacin da ta Ruga a guje ba tare da Rungumeshi Farincikin da take ciki tama kasa musaltashi da komai Kuka ta fashe dashi cikin muryar kuka ta ce ……….✍🏿
“`Hmmmm ya kukaji salon Fans kudai muje zuwa ai ba afara komai ba salon na musamman ne Kudai kawai Had’in kanku nake buk’ata ta hanyar comment da zazzafan sharhi ni kuma zan datse damtse wannan Karin ba wasa a zafafe na dawo kamar yanda littafin yake zazzafa Idan Naji comment da sharhi zaku jini idan kuma Naji shiru nima zaku jini shiru ta hanyar yawan comment ne zan gane labarin zai muku dadi ko akasin haka more comment more typing “` 💪🏼🤷🏼♀️🙅🏻♀️
_*Miss Hajo ce*_
[5/23, 18:16] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏
Hot love story♥️🔐
“`MALLAKAR“`
*Hajara L Sadeq*
📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚
بسم الله الر حمن الر حين
*BOOK ONE*📔
🅿️……………3&4
“My Yaya why did you turn off your phone for two days i could not find you’’ dad dab’a bayanta yafara cikin sigar lallashi ya ce “ I’m sorry my cutie Babe bansan zaki tashi hankalinki haka ba I did this to surprise you shiyasa “sakinshi tayi tare da turo baki ta ce ‘’uhm My Yaya ni nayi fushi ma tunda da gangan kayimun haka ‘’ta turo baki ta koma kan Kujera ta Zauna ta na turo baki ita ala dole anyi mata laifi”Murmushi yayi tare da binta dan yasan ya tab’o y’ar rigimar tashi kamar zaiyi mata rad’a ya ce.
“Sorry my cutie bazan sakeba kinsan fa duk saboda naganki na dawo kiyi hakuri ki janye fushin kinji little sis”Turo baki gaba tayi ta ce “Ni bazan hak’ura ba “kamar zaiyi kuka ya ce “Too na koma chan kenan “juyowa tayi cikin sigar shagwab’a tace “nayi missing din naka shine zakace zaka koma “ta fad’a ta na aika mashi da hararar wasa lakutar kumatunta yayi yace “Nima kewarki ce ta dawo dani I was joking dan ki hakura “To ai nahakura karka sake “murmushinshi mai tsada ya sakar mata ya ce insha Allah bazan sakeba smile mana kinsan kinfi kyau da murmushi “Dariya tayi tare da rufe fuska ta kwance kanta saman kafadarshi sai sannan yayi ajiyar zuciya yace”fatan dai na sameki lfy”gyada mashi kai ta yi tace “Alhmdllh saidai rashin lafiyar kewarka kuma yanzu na warke hope kazo lafiya ya hanya “murmushi yayi yace Nima lfy nadawo sai dai cutar kewarki kuma yanzu na warke ya fada yana shafar kanta ya ce “kinga yanda kika kara girma kuwa cutie Meye sirrin ko dai inna wani abun take baki “.
Dariya tayi tare da rufe fuska tace “Kai yaya ai kaine ma ka kara girma “Tsinkayi murnar inna sukayi “To fa jarabar ta dawo yanzu za a faramun manne manne da tab’e-tab’e a daki ta karasa fada ta na jan tsaki “Dariya duka sukayi Banda Arman da baifiya dariyaba murmusawa kawai yayi ya ce .
“Haba y’ar tsohuwas daga zuwana bako sannu da zuwa bakiyiwa angon naki ba zaki fara halin “tabe baki tayi ta ce “Akai kasuwa indai kaine sannan daka shigo ko gaisheni bakayiba bama ka ganni a wajenba ka tafi wajen fitsararriyar y’ar lelen naka “murmushi yayi yana kallon Aira yanda take aikawa da inna harara yace “afuwan hajjaju Nina isa na kyale uwar gida ran gida Allah huci zuciyarki ran ki ya dad’e kiyi shekaru irin na dabino “lokaci guda inna ta saki rai ta ce “sannu da zuwa Mujahid ya kasar turawan andawo lafiya “lafiya qlau inna fatan kuma mun sameku lafiya “su Amma ne da Haidar suka gaisheshi ya amsa a tak’aice basu damuba saboda daman sunsan duk gidan nan ba wanda yake sakewa ko doguwar magana ta hadasu sai Aira.
Aira ce ta ce “Yaya ka rabu da inna Neman fitina ne kawai irin nata kaga tashi ma mu fita na baka labarin abubuwan da Akayi Baka nan ta fada ta na mikewa tare da kama hannunshi sukayi farfajiyar gidan Sunajin inna na sababi suka kyaleta.
Sun jima a waje suna ta Hira ta bashi labari na dariya yayi itama haka har akai margriba suna nan saida Mummy ta kirashi ya Sanyashi tunawa da ta ce kar ya jima yace mata yanzu zai dawo kallon Aira yayi ya ce “Baby zanwuce Gida Mummy na kirana “nan ta fara shagwaba ita bata gaji da ganinshi ba dakyal ya samu ya lallabata ya tafi gida da niyyar washegari zai dawo yakaita shan ice cream kuma zai taho mata da tsarabarta.
Daren ranar kowannensu Kwanan farinciki yayi Washegari Aira koda ta dawo daga school Lokacin Tahfex nayi langwabewa tayi tace batada lafiya bazataje ba saboda kar Yaya Arman yazo ta tafi.
Da misalin karfe biyar na yamma ya shigo gidan sosai yayi mata kyau cikin riga ash da black din jeans itama tayi kyau cikin atamfarta doguwar riga ta sa malha tayi daurin dankwalinta tare da fito da gashinta baya sosai tayi kyau Arman ko kasa daina kallonta yayi dan ba karamun kyau tayi mashi ba bayan ta shigo gaban Motar ta ce “Yaya na shirya muje ko”Harararta yayi yace a haka zakije gashin kanki duk waje kuma wannan miririn mayafin zaki yafa jeki ki sanyo hijab “kamar zatayi kuka tace “Dan Allah yaya ka bari muje harfa na shirya kuma idan na koma inna ganewa zatai da inda zamu bakaga gyalenma a jaka na sanyashiba “zakija a fasa fitar wlh muddin haka zaki fita gardawa na gane maki gashi ke ko kishin kanki bakyayi “Yafa gyalan tayi ta saman ka tace “to yaya na rufe kan please karka kara cewa wani abu “badan ranshi yasoba suka tafi dan yana bakin cikin mutane su dinga ganemishi surar Airar shi ba danshi kad’ai yasan kalar so da kishinta da yake “.
Wuraren shakatawa sosai yakaita sai murna da farinciki take tabbas farincikinta yadawo rabon da tashiga farinciki haka tun tafiyarshi london kimanin wata biyu kenan.
A hanyar su ta dawowa a mota ya bata kyautar hadaddiyar zoben gold din daya sayo mata sosai tayi farinciki da murna sai godiya takemai shidai murmushi kawai yake yana kare mata kallo.
Suna isa suka fito Hannunsu makale da na juna sai Dariya take ta farinciki tana zabgamai godiya daidai zasu shiga palourn inna Abba na fitowa Sosai gabanta ya fadi cikin dabarbarcewa ta fara kokarin kwace hannunta ya rike gam tare da galla mata harara kamar zatai kuka tace ka sakeni kara rike hannunta yayi ma .
kallon zaki gane kuranta Abba yayi mata tare da wucewarshi sosai nayi mamakin ganin Arman baiko gaishe da Abba ba saima kauda kai da yayi Abba na wucewa Arman ya gallawa Aira harara yace “ita kuma wannan rikicewar da kikayi ta mecece kamar kinga mala’ikan mutuwa “cikin muryar in ina tace yaya ab ba tsaki yaja tare da sakin hannunta ya wuce ya fasa shiga gidan inna durkushewa tayi ta fashe da kuka tasan ba karamun hukunci zata fuskanta a wajen Abba ba ga kuma shima yaya Arman din yatafi kamar fushi ma yayi da ita tana cikin kuka haidar yazo tare da daddabata ya ce “ya Aira Abba yace kizo yanzu yanzunnan ki sameshi a babban palour kika wuce minti biyar kinsan sauran……….✍🏿
Tofa meye dalilin da yasa Aira ta rikice ganin Abba ya ganta tare da Arman ????
Meye dalilin da yasa Arman bai gaishe da Abba ba????
Tukunnama wace Alakace ke tsakaninsu????
Zaku samu amsarkune ta hanyar bibiyata cikin wannan zazzafan labari
* Ta hanyar comment da sharhi tare da sharing shine abunda zaisa na gane labarin yana muku dadi ko akasin haka kuma shine babbar kwarin gwiwar da zaku bani idan kun karanta ku dinga comment tare da sharing sauran grps masoyan asali*
[…] Ni da Yaya Arman Hausa Novel Complete […]