Littafan Hausa Novels

Halin Rayuwa Hausa Novel Complete

Written by Hausa_Novels

Halin Rayuwa Hausa Novel Complete

 

 

 

 

 

 

 

 

HALIN RAYUWA

 

1

 

 

NA

 

07035586299

 

HAJ. HAFSAT C. SODANGI

 

(Mrs Yunus Abdullahi Dabai)

 

1

 

 

 

Hakkin Mallaka [m]

Hakkin Mallakar littafin na Haj. Hafsat C. Sodangi ne

 

GODIYA

Godiyata har kullum ga Allah take Subhanahu

ta’ala mai kowa mai komai, Makadaici, Mahalicci wanda a ke nufa da dukkan bukatu gwani mai hikima wanda yayi halittarsa bisa tsari na aure wato mace da namiji.

Tsira da aminci su kara tabbata ga cikamakin

Annabawa, shugaban Manzanni Annabin karshe

Muhammad (S.A.W) da alayensa da sahabbansa da

wadanda suka bi ma tafarkinsa na gaskiya har zuwa

ranar karshe, wato ranar rarrabewa tsakanin karya da

gaskiya (AIkiyama), Ubangiji yasa mu dace.

Har wayau ina mika godiyata ta musamman ga

daukacin makaranta littattafaee cikin kasa da waje,

Ubangiji ya saka da alheri ya kuma kara karfafa

zumuncin da ke tsakaninmu.

 

Na gode, Haj. Hafsat C. Sodangi

6/7/1434

 

GODIYA

 

Godiya mai dumbin yawa gare ki.

Rabi’atu Faruk Jauro (Ministry of Commerce and

Industry Yola, Adamawa State) Da Zainab Sunusi Kofar

Gabas Danbatta, Zainab Abarshi Yawuri

2

 

HALIN RAYUWA

A duk sanda naci karo da wata kalma da

ta danganci rayuwa gabana kan fadi in

tsinci kaina cikin wani matsayi na tsoro da

razana, wani lokaci ma in ji na samu kaina cikin

halin da zuciyata kan samu kanta cikin yanayi na

kaikawo saboda tunawa da al’amuran da suka

shafi jiyana da yau dina, in suke jin wani

mummunan faduwar gaban idan na tunan ba ni

da tabbatas ko masu niya bisa gobena.

A mafi yawancin lokaci kuma in har nayi irin

wannan tunanin to nakan samu kaina ne da yiwa

gwanin halitta godiya da bai sanya mana wani

tabbataccen al’amari ba in dai cikin wannann

rayuwar tamu ne ta wannan dunyar, duk abinda

ka gani zai wuce.

Farin ciki ko bakin ciki yana da lokaci, komai

yayi farko wata rana zai yi karshe. Wani karin

maganar ma sai ya ce abin da ya baka tsoro a yau

babu mamaki gobe ya baka tausayi, wasu ma da

suka yi wa rayuwa irin fahimtar da suka yi wwa

rayuwa irin fahimtar da suka yi mata sai suka ce

wai ita din tamfar hawainiya ta ke, ta kan iya

canza launinta a kowane lokaci.

Al’amuran da na gani a shekaruna na

kuruciya sun sanya ni son bayar da labarina ga

na kasa dani ba don wani labarin dadin bayarwa

 

3

 

 

 

ke gare shi ba, a’a sai dai don ya zamo hannunka

mai sanda a gare su. Ya zamo musu wani darasi

da za su rika don su kauce daga aikata kurarai

irin na kuruciya kurarai da kan zamo tanfar na

tsalle daya mai jefa mai shi rijiya.

Wannan labari da nake nufin bayarwa a yau

labari ne da ya danganci halin da rayuwata ta

kasance shekaru talatin baya da suka wuce a

lokacin da na ke da shekaru tara kacal a duniya.

Ni Maryam Abubakar, na taso ne a gidanmu

gaban iyayena uwa da uba cikin gata kulawa da

kuma tarbiya, a wantcan lokacin da nake magana

a kai iyayena uwa da uha suna matukar sona

musamman ma Babana wanda Sunan

Mahaifiyarshi ke gare ni bisa hakanne ma bai

fadin sunan nawa sai yake kirana da kalma ta

Yacuwuna’ kalmar da ke nufin ohaifiva ko

uwa cikin harshen barbarci.

Wani dalilin da ya kara tsananin soyayyarshi

gare ni ko in ce muni da Yayata Khadija wacce

take ta girme ni da yawa, don a lokacin da nake

da shekaru. taranne a ka yi bukinta da wani

saurayinta da suka so juna tun suna ‘yan yara,

Ibrahim shi ne din bai da kowa sai mu, nai da

dangi ko kuma in ce ya dade rabonshi da yayi

mu’amalla da su ba ya ma maganarsu.

4

 

 

Nasha jin Innata a wancan lokacin tana ce

mishi Mallam ko ba don mu ba kai ni wurin ‘yan

uwannan namu in gano su saboda yaran nan su

gansu su ban iyayensu da danginsu saboda in mu

ne yau ba mu ne gobe ba, su kuwa dangi

musamman na uba ko don maganin gori a neme

su.

A mafi yawancin lokaci ta kan yi irin

wadannan maganganunne har ta gama ba tare da

ya tanka mata ko ya ce mata uffan ba. Sai dai

wannan bayani da nayi a kan Babana bai hana

shi zamowa daga cikin mutanen kirki ba, mutumn

ne mai tsananin hakuri mai gudun bacin ran

wani, mai girmama makwabci wanda ba ya shiga

harkar da ba tashi ba, ba mai yawan magana ba

ne mafi yawancin lokaci hirarshi takan yi nisa ne

kawai da makwabcinshi Mallam Hodijo wanda

suka zama tanfar yan uwa shi da shi ga shi

kuma sai aka yi dace Babana Babarbare ne

wanda ko zanen da ke fuskarshi ya isa ya

bayyanar da asalinshi.

Haka shima Mallam Hodijo Bafulatani ne da

bai bukatar sain an tsaya bayani a kan shi, don

haka sai abin nasu ya kara zamowa gwanin

sha’awa kullum a cikin zolayar junansu suke

suna raha tare da barkwancin wasan fulani da

 

5

 

Barebari, haka kuma alaka take tsakanin Innata

da matar Mallam Hodijo mai suna sumaye.

Wani dalilin da ya karawa Babana sonmu ni

da ‘yar uwar tawa shine, kasancewar matarshi

mata mai wabin ‘ya’ya cikin haihuwa bakwai da

aka yi ne aka samu mu biyun muka rayu.

Rashin sanin dangin Babana ko rashin

mu’amallar da su bai hana gidanmu zamo wa

gidana Jama’a ba Innata mai ‘yan uwa ce ban da

haka kuma mata ce da ta iya mu’amalla da

mutane da ke kuma iyakacin kokarinta wajen

kiyaye hakkin makwabtanta.

Ita din kuma mata ce da yawan mu’amallarta

da ‘ya’yan da ba nata ba, ya zamo dalilin da ta

zamo uwar yara da yawa maza kuma da mata

kanana da kuma ‘yan samari.

Gwanar kitson ce da kuma lalle bata laima da

kwiya kan hakan sannan bata taba damuwa dayi

don a biya ta ba, don haka kullum ta zaunar da ni

da nufin yi min kitso ko lalle to zata hada ne da

duk yaran da muke wasa da su a wannan lokacin

tayi mana kitso da lallen tare da wannan dalili sai

tayi sabo da iyaye da yawa na yaran da take yi

mana kitson nan ko lallen tare wasu daga uwa

godiya bayan sun aiko mata da abin hasafi ta

mayar su biyo baya.

 

6

 

Wasu yaran da ta zamo uwa gare su kuma

musamman yan mazan daga yawan ciyarwarta

ne tana ganin yaro cikin wani zata zaunar da shi

ta zuba mishi abinci in har ya yarda yaci zata

gaya mishi gobe ma kazo daga haka har sai zuwaa

wurin nata ya zame mishi jiki ko kuma dabi’a,

don haka a ko ina yara suka ga Inna za ka ji suna

Mama’ Mama ina za ki? Mama kin dawo?

Mama kin ga wane ko? Hatta wasu iyayen yaran

da suka san Inna uwa ce a wurin ‘ya’yansu, za ka

ji suna gaya mata laifin yaran nasu don nufin ta

taya su yi musu fada kan laifuffukan nasu kko

kuma kin da suke yi wa makaranta.

Cikin yaran da Inna ke yin mu’amallah mai

karfi da su akwai Mubarak da Mansur wadanda

su ba suna zuwa wurinta don cin tuwonta bane

a’a sukam ma yan gata ne a gidajensu

musamman Mubarak wanda shi shi kadai ne da

namiji a gidansu a wurin kuma ubanshi Alhaji

Mühammadu wanda a unguwar tamu duka babu

maigidan da ya kai nashi girma da kuma kyau.

To haka shima Mansur ko da suke da yawa a

gidansu gidan nasu na rufin asiri ne, su suna

zuwa wurin Inna ne kawai saboda gidannata ya

zamo wurin zuwan yaran unguwar har kuma sai

ka ji suna tambayarta Mama da wani abu ne mai

dan dumi in akwai ta ce akwai in babu ta ce sai

7

Raino ne sila Hausa Novel Complete

 

garin rogo, wani lokacin ma har sai ka ji tana yi

musu fada kan abin da tasan suna yi musamman

Mubarak, kusan kullum ya shigo za ka ji tana

tambayarshi kaje Makarantar ko yau ma ba ka je

ba? In yaje ya ce yaje in bai je ba ya dan tsuke

fuska yana yi mata bayani Mama ke ba za ki

gane ba ne? ta ce Eh, ba zan gane ba in ba ka

gaya min damuwarka ba amma in har za ka bude

baki ka gaya min ai zanfahimci daidai

gwargwado, tayi mishi nasiha

lyayena ba masu hali ba ne, amma a cikin

rufin asiri muke rayuwarmu, sana’ar Babana

sana’a ce ta rufin asii, kayañ miya yake sayarwa

a saman layinmu ba sni da tsawwalawa.kan

kayanshi, don haka wurin nashi matattara ce ta

cinikin yara.

Mallam ban tumatir, Mallatu han attarugu,

Mallam ban alayyaho, aikin ke nan. Don naka

inhar ban je Makaranta ko gidan Yaya Dijah ba

to yawanci na kan je wurinshi ne in rinka taya

shi in yana bada kaya in rinka karbar mishi kudi

saboda wasu yaran da tarbiya bata ishe su ba

sukan karbi kayan miyan su tafi ba tare da sun

ba shi kudin ba saboda ganin hankalinsi ya tafi

wajen masu kokarin ya ba su nasu.

Babana ba mutum ba ne mai dogon buri ko

mako game da kudi, don hakan kullum ya dawo

 

8

 

daga kasuwarshi ya kan tattara duk cinikin nashi

ne ya mika mata ko kuma ni ya miko min in

shirya su in je in ajiye su a inda nasan tana adana

kudi.

Shi kuma ba mai yawan sa ido kan abubuwa

ba ne, balle ka ji shi yana kididdiga ko tuhuma,

don haka kusan komai Inna ce take tafiyarwa

tana ganin wani rami a çikin gidanmu za ka ji ta

kira wani daga cikin samarin da suke shigowa

wurinta ta basu kudi ta ce maza suyo siminti ka

toshe mnin wannan wurin.

In kwata ce take nema ia cika zata sa su nemo

mai kwasheta ya gyara suyi ciniki ya kwashe ta

basu kudin suje su biya haka nan rufin kwano in

ta hango alamar zuwan damina zata basu kudin

foti su sayo su nemo mata mai hawa kwanon ya

kara bin kusoshi da fotin din maganin yoyo.

Haka nan kuma ko wata hidima ce ta taso

bata jiran Babana sai dai ta ce mishi an yi kaza

an yi kaza ko da kuwa ta sallah ce ko azumi ya

ce mata to, ko da kuwa a kan shi ne zata yi tayi

mishi tuni musamman da sallah, Mallam in fa

baka sayi yadi ka bada dinkinka yanzu ba zaka

rasa dinki, ya ce mata to don na rasa dinki

menene tunda dai ke da yaran kun samu ai shi ke

nan.

 

9

 

 

Tayi murmushi ta ce, Haba Mallam ana

hidimar sallah ai zan so nima in ga mijina fes in

Rara jin dadi da yiwa Ubangiji godiya, yayi

kamar bai ji ta ba. Inna da makwabciyarta Babah

Sumaye wani irin zama suke yi da yafi na ‘yan

uwan da babu fahimta da kauna ta zumunci a

tsakaninsu dadi.

Kusan kullum sai wata fa shigo wurin wata

duk abin da suka girka sai sun aikewa juna, wata

rana ma ka ji daya tana cewa dayar in za ki yi

girki kiyi tare da nan gidan, don kasala nake ji ko

kuma aiki zai yi min yawa-za a yi abu kaza da

kaza su ce to.

To haka Babana yake da mallam Hodijo

ko’ina za su suna tare ko da kuwa Masallaci ne

kullum kuma naje karbo cefanen gidanmu, to

nakan hado ne da na gidan su Babah Sumaye.

Innata ba wata jaruma ba ce in dai a kan

neman kudi ne bata da wata sana’a da take yi ta

maida taro ya zama sisi anima tana cikin wadata

saboda halin mijinta na komai nashi a wurinta

yake ajiye shi bai da kuma matsala don ta ce

mishi ta kashe kaza kan abu kaza na hidima da

ya taso haka nan ita din gwana ce kwarai ta

shirya abinci mai dadi aci shima Baban nawa

mai son cin dadin ne.

 

10

 

 

Sannan ta iya zama da shi ta iya tarairayarshi

da tattalinshi duk da shi ba mai yawan magana

ba ne, ko yawan dariya amma in suna tare shi da

ita fuskarshi bata rabo da murnmushi, bini-bini

kuma za ka ji shi yana yawan ambaton sunanta

Ramatu.

Gidanmu karamin gida ne dan madaidaici,

dakuna hudu ne a ciki, ciki da falo guda daya

wanda ni da Inna muke ciki, sai dai-dai guda

biyu, daya Babana daya kuma tarkace na

kwandunan tumatir din Babana da sauran

kayayyakin Inna na aiki, kullum ka shigo

gidanmu daga zauren gidan ka ke soma shakar

kamshin turaren Innata.

Ana cikin hakanne aka wayi gari a gidan

namu Inna tana wani irin rashin lafiya da Babana

yayi ta zarya yayi ta zirga-zirga da dawainiya

mai yawa a kai, cikin wani irin farin ciki da

zumudi mai yawa.

Haka nan itama Babah Sumaye tayi ta hidima

aikin gidanmu gaba daya ya zama nata, ta rinka

kai kawo tana ta faman murna ashe, ashe wai

Innar tawa wani cikin ne da ita, ni kam nayi farin

ciki saboda ganin zan samu kani wata kila mace

watakila namiji, wanda dama nasan Babana yana

Son samunshi.

 

11

 

Sai dai kuma gabana ya fadi da na tuna da

irin haihuwar da Innan tayi shekara guda da ya

wuce inda ta kubuta da kyar.

Kankana, abarba, lemo da ayaba basa

yankewa a gidanmu, saboda kullum sai Mallam

Hodijo ya kawo ya ce a kawo mata saboda abin

sana’arshi ke nan a bakin asibitin garinmu.

Haka a ka yi ta fama da ita har dai ta samu

sauki ta wartsake ta koma kan al’amuranta.

Muna nan a haka har cikin Inna ya bayyana

ya fito sosai, dama kuma ita din mai katon ciki

ne ina jin ta rannan a hirar da suke yi tana gaya

mishi ni dai ban taba jin ciki irin wannan ba

Mallam, ko kuma don mutum ya fara girma ne

yake jin hakan oho.

Yayi murmushi ya ce, “Ramatu ke nan, kina

yar shekaru talatin da biyar kina gayawa kanki

girma da kuma ni ne nayi kuskuren ba ki nace

miki kin girma da kin ce.na hango wata yarinyar

ne a waje yáa sani kiranki tsohuwa.”

Tayi murmushi ta ce, “Uhun! Mallam ke nan,

to tunda a ka yi auren yarinyar nan kuwa har

gata yanzu da juna biyu ai dole in kirawa kaina

girma ni da kaina.”

Ya tayata murmushin kafin ya sake kallonta

Cikin natsuwa ya ce mata, ai ba Dija ce mizanin

da za ki rinka dubawa wajen gane girmanki ba,

 

12

 

ni za ki rinka dubawa ai ni ne ma’aurinki ya ya

ki ke a wurina? Shi ne maganarki, ya ya nake

kallonki? Shi ya kamata ya zama abin lurarki,to

in kuwa ni ne ban taba kallonki na gane

canzawarki ko bambancin da ke tsakaninki a yau

da na ranar da mahaifinki ya kira ni ya ce min in

dawo da yamma inga ‘yar da yake da ita in tayi

min in kawo sadaki a daura min aure da ita babu

wata rana da nake wayar gari ko zan wayi gari

ban yi wa wannan mutumin kirki addu’a ba

Ramatu.”

Ta kalle shi ta dan yi murmushi ta ce, Uhun

kai Mallam babu halin in kawo maka wata

magana sai ka kawo wannan zancen ya ce, Eh ai

bana gajiya da bada labarin ne saboda ya bani

abin da ban taba tsammanin samu ba na kar6i

aurenki cikin tsananin tsoro saboda nayi zaton za

ki bijire sai kuma ki ka zamo yarinya mai

albarka mai ladabi da biyayya, mai sanin darajar

iyaye da aurenki.

Tunda ki ka zo wurina ban taba ganin wani

al’amari daga gare ki ba sai na alheri.” Shiru

Inna tayi tana sauraronshi sai da ya gaji ya canza

zancen don kanshi ni nafi zaton canjin da kike ji

din wata kila da namiji ne ai kin san gaba daya

haihuwar nan da a ka yi in ban da na farin sauran

 

13

 

shidan duk mata ne amma tunda kin ce kina da

damuwa to tashi kawai muje asibiti.”

Tayi maza ta ce ka ji Mallam kuma shekaran

jiya ne fa naje awo suka kuma ce min babu

matsala, iyaka dai in dan rage cin gishiri da

barkono.”

Haka rayuwar Inna da Babana take kullum a

cikin ganin alherinta yake, bai daga ido ya kalli

wani al’amarinta ba balle ya gano kuskurenta

baida wani labari wanda ya wuce na fadin

alherin mahaifinta saboda ba shi ita da yayi ba

tare da shi din ya neme ta ba ya kuma ba shi ita

tana da shekaru goma sha biyar a duniya, bayan

kuma gata da manema masu yawa da suke fatan

ganin an ba su aurenta.

Kullum Babana a cikin sayayyar haihuwar

Inna yake komai ya gani ya bashi sha’awa zai

sayo yazo da shi gida, rannan ina jin ta tana ce

mishi wannan kayan fa Mallam yawansu ya isa

haka.

Kuma ma ni sai nafi son a hakura da sayayyar

haka sai an ga an yi haihuwar tukuna saboda ni

dai Mallam zuciyata a tsinke take game da

haihuwar nan.

Yayi maza ya dago ido ya kalleta za ki fara

ko Ramatu? Kin san irin fadar min da gaban da

kike yi kuwa idan kina furta irin wadannan

 

14

kalaman? Kin sani sarai ai kin uma san abinda

kike yi in yi kike yi don in ji dadi kin sani, in ma

don me kike yi kin sani.

Kin sani sarai bani da kowa bani kuma da

yan ‘ya’yannan naki amma sai ki rinka gaya

min maganganun da zan rinka hawa gadona da

daddare ina kasa yin bacci saboda lissafe-

lissafen al’amura. Tayi murmushi ta ce, “To kayi

hakuri Mallam bari in je in kawo maka

abincinka.”

Bai saki fuska ba ya ce, To wane abinci kumna

zan ci ni yanzu bayan kin gaya min wannan

maganar.”

Ta sake yin wani murmushin ta ce, “Kayi

hakuri Mallam ba zan sake yin ba amma da

wannan katon cikin nawa da wannan kwalliyar

da nayi don ka ji dadi in girka abinci don kai ka

ce ba za ka ci ba ai kai ma kasan in na soma

fushi zan dade ban huce ba, burabusko fa nayi

maka da miyar yakuwa, ta kuma sha kashi da

tantakwashin ga kuma nama ka gani?”

Ta zauna kusa da shi tana nuna mishi in zuba

maka? Ya ce To ko don tsoron kar kiyi fushi ai

zan ci Ramatu amma in don yunwar da na dawo

da ita ne ai ta tafi tunda taji irin kalaman ki tayi

maza ta ce ai ba zan sake ba kayi hakuri ya ce ya

wuce Ramatu.

 

15

 

Anyi hakan bai dauki wasu kwanaki da suka

zamo masu yawa ba na farka cikin dare naga

kofar dakin Innata a bude alhalin sanda zamu

kwanta ni da hannuna ne na rufe kofar har na

sanya mata salanta nayi kamar in gyara ruhuwata

da na fahimci zamewanta ne yayi dalilin

farkawar tawa saboda tsananin sanyin da a ke yi

har na juya da nufin komawa baccina sai kuma

na tuna ai ban ga Innata a wurin kwanciyarta ba

da sauri naji baccin ya sake ni nayi mika na bude

idanuwa sosai a kasa na ganta a durkushe da

gwiwoyinta a kasa ta dafa wata kujera ‘yar

tsugune wacce dama ta zamanta ne a kicin

nantake na karan wartsakewa ina kara bude ido

don in ganta da kyau har nayi nufin saukowa in

da take sai ga Babana ya shigo dakin cikin sauri

rike da kwanon sha karami a hannunshi alamar

rubutu yaje ya yiwo mata daga wannan rubutun

dai Ramatu in bai yi ba sai kawai mu tafi asibiti

kin ga nakudar tayi tsawo kar muzo muyi irin na

wancan karon shima asibitin yana da amfaninshi

ai duk rama ce ta Ubangiji ta kawomasu bata dai

tanka ba.

Ya isa gare ta ya durkusa a gabanta shi ma

kan gwiwoyinshi karbi ki sha rubutun nan

Ramatu, bata motsa ba daga yanayin ta na

 

16

 

sunkuyar da kan da tayi tana kallon ‘yan

yatsunta.

A hankali cikin matsananciyar taushi da

laushin murya ta ce mishi ka yafe min abubuwan

da nayi maka Mallama.

Ya kara zuba mata ido watakila ba wannan

ne karo na farko da tayi mishi irin wannan rokon

ba saboda jin da nayi ya ce mata, To ni wai me

kika yi min ne Ramatu da ki ke ta nanata min

wannan maganar? Ai ni ban san komai ba game

da ke in ban da alherinki shekaru ashirin din

aurena da ke sune shekaruna na jin dadi da

samun farin cikin rayuwa in ban da ke da wata

kila ban taba sanin jin dadi ba, na zauna da ke

kina yi mini biyayya kina tattalin farin cikina,

kina kyautata min, ban taba yi miki umarni kin

ki bi ba, ban taba cewa ga yanda za ki yi kin ce

a’a ba.

 

A kullum ckin kiyaye bacin raina ki ke, to me

zan ce miki? In har akwai abin da ki ke yi min da

ki ke kuntatawa rayuwata ai bai wuce irin

wadannan kalmomin naki ba, tunda kin san me

suke nufi a gare ni, kina yi min nuni ne da zan

iya komawa in da na baro har gara ma wancan

lokacin ban taba danddanar wani madandani da

ya kwadaitar da ni son rayuwar duniya ba kamar

yanzu, to suma na yafe miki tunda nasan kina

 

17

 

cikin wani hali ne yasa ki ke yi mini hakan.

Ubangiji ya raba ki da wannan ciki lafiya.

Ni da nake kwance shiru a kan gado nake ta

faman kukan sharbe na kasa saukowa daga kan

gadon saboda tsoron kar a ce min in fita waje ba

wai don tsoron daren ba sai don tsoron kar a

hana ni ganin halin da Innata ke ciki saboda

nasan a duk lokacin da Babana ya shigo dakin

Innata ba a barina in shiga in ma ina ciki zan yi

sauri in tashi in fita tunda nasan ko ban yi hakan

ba ita Innan zata sani ni ce cikin zuciyata na

amsa addu’ ar tashi na ce amin.

Mallam yayi maza ya ce na’ am Ramatu me ki

ke son 6aya min? me ki ke so in yi miki? A

hankali ta ce mishi Mama ce. Gabana ya yanke

ya fadi jin ta ambaci sunana. Cikin natsuwa ya

ce mata “Eh, me Maman nawa tayi?

Ta sake rage murya kafin ta ce mishi, ka

baiwa Innata rikonta zata rike maka ita kamar

ina raye.

Cikin nutsuwa ya ce mata, In har ina raye to

a’a duk inda zan shiga zan shiga ne tare da ita,

zata rage min kewarki yayi maza ya share wasu

zafafan hawaye da suka zubo daga idonshi. Ita

din ai kama da ke take yi, kina raye ma nakan

kalle ta in yi mamakin kamanninta da ke balle

kuma in kin tafi kin bar ni.

 

18

 

Wasu hawayen suka ci gaba da zubowa daga

idanunshi har suna jika rigarshi, ban taba yi miki

karya ba, ba zan yi miki a wannan lokacin ba,

zan dai yi miki alkawari a duk lokacin da na

hango wata alama ta katsewar rayuwata, to cikin

taimakon Ubangiji zan mika mata ita.

Yana gama fadin hakan yayi maza yà miko

wata Jaka ya dauko wacce yasan nan Inna take

tara kayan haihuwarta yana cikin haka sai ga

Babah Sumaye da Baba Hodijo sun shigo alamar

kofar gidanmu ma a bude take sun kuma san da

abinda Inna ke ciki.

Mallam Bukar ga motar nan fa a waje mun

samota, da sauri Babana ya ce, To mu tafi.”

Yasa hannu ya daga Inna ya tsaida ita, Babah

Sumaye ta daura mata zani tana fadin “Iko sai

mai shi.” Gaba daya cikin ya tattara ya dawo

kirjinta.

Tuni na sauko daga kan gadon ina ta faman

kuka ina rike da hannun Innata wacce itama ta

kama nawa hannun ta kankame a cikin nata.

“Sake ta mu tafi, muje ki shiga gida ki samu

Jumare ku kwanta tare tazo tana nan a ciki, ki

kuma daina wannan kukan da ki ke yi, kiyi mata

addu’a kawai in Ubangiji ya kawo saukin

lamarin da sassafe sai ki ga mun dawo tare da

 

19

 

sabon yaronmu ko yarinya. Ki samu wata ‘yar

uwar.

Wadannan duka kalaman Mama Sumaye ne

don haka na dan samu natsuwa har na wuce na

shiga cikin gidan nasu naje na samu Jumare

muka kwanta mu kuma namu gidan aka sa

kwado a ka kulle shi.

Jumare ‘yar kanwar Babah Sumaye ce da ke

yawan zuwa wurinta, ta girme ni da shekarun da

suka kai hudu, don haka ta fini wayo tana ganina

ta ce min ke share hawayenki kizo muyi

kwanciyarmu haka ake yi in za a haihu gobe za

ki ga sun dawo da sabon yaro ko mace ko namiji,

wanne ki ka fi so?

Na dan yi shiru wai zan yi zabi, nan da nan

kuma naji bani da wani zabi bana ma dokin

abinda za a haifan tunda naga wahalar da take

ciki, bukatata kawai in ganta ne ta dawo gida

lafiya.

Duk da kalaman da aka yi min na Inna

haihuwa zata yi ba daga kwanciyata nayi bacci

ba saboda na riga na tsorata da abinda na gani,

daga baya ne kawai da yake shi bacci 6arawo ne

ya sadado yazo ya dauke ni.

Farkawa nayi daga baccin nawa a dalilin nayi

ya ishe ni ga kuma hasken rana da ya cika dakin

da sauri na diro daga kan gadon na fito dakin da

 

20

 

gudu, gidanmu nake nufin zuwa inga o zanga

Inna da sabon yaron da aka ce kan safiya zata

haife shi Jumare na gani a zauren gidan ta rabe

tana leke.

Nima na tayata yin leken don in ga abin da

take gani, cincirindon jama’a ne gaba dayansu

kuma maza babu mace ko daya gashi kuma

yawan nasu yakai inda ya kai.

Can gefe ga yara ‘yan saffa suma maza mafi

yawancinsu kuka suke yi. Da sauri na kalli

Jumare meye a ke yi? Ta kara lekawa tana

kokarin tantancewa kamar fa rasuwa a ka yi

amma ban sani ba.

Muna cikin haka sai ga makara an fito da itaa

daga cikin gidanmu da mutum shimfide a ciki,

ina kallo a ka yi sahuana sallar amma wai ban

gane Innata ce a ciki ba, ina ji Jumare tana gaya

min wanda ya rasunne a ciki, na kuma ga zanin

Innata lullube kan likafanin amma kwata-kwata

ban kawowa kaina cewar ni ce na rasa Innata ba

saboda ban taba zaton zan rasata a wannan

lokacin ba, ban taba zaton zata daukan min

mahaifiyata ta raba ni da ita kamar yanda tayi wa

daruruwan yaran da ba za su kidayu ba.

“Waye ne ya rasu Jumare? nayi tambayar

cikin tsananin tsoro da firgita ba wai don ina

zaton abin ya kasance ne a kan Innata ba, sai dai

 

21

 

kawai don naga abin da ban taba gani ba, wanda

kuma yayi matukar tsorata ni.

Na sake yi mata tambayar mai yawa na sake

yi mata tambayar da sauri ta ce min, “Ke ban

sani ba. Saboda itama ta shiga wani yanayi na

kuma yarda har a yau dinnan na yarda Jumare

bata san Innata ake sallata ba.

 

Ban san yanda aka yi ba ina ganin an dauki

makarar nan an tafi da ita din, bin Jama’a sun bi

bayanta cincirindon yara suka yi ta dalewa kan

manyan motoči za su bi don yi mata rakiya na

kama kuka sosai da sosai Jumare tana bani

hakuri.

Daga baya ne kawai na soma jin matan da ke

wucewa ta bayangidan za su shiga gidanmu,

suna fadin “Ikon sai Ubangiji! Ashe Ramatu ce

ta rasu?

Ban san yadda a ka yi ba, ganina kawai nayi a

cikin gidanmu Yaya Dijah tana kankame dani a

jikinta tana ta faman kuka, bai yiwuwa in tsaya

kwatance ko bada labarin abinda ya faru. illa

iyaka dai kawai an yi zaman makokin Ina na

kwana uku cikin matsananciyar kewa da jimam

da addu’o’i ba daga wurin mu ya’yanta ko

mijinta ko danginta ba kawai. Har daga wurin

Jama’a masu yawa da suka santa ko suka Ji

 

22

 

labarinta wurin kira da mutanen da suka san

rayuwarta.

An watse daga zaman makokin Inna, ‘yan

uwa da abokan arziki duk suka watse aka bar mu

daga mu sai mu a gidanmu, ina nufin daga

Babana sai ni sai ko Yaya Dijah da take nan bata

koma dakinta ba.

Muna zaune gaban Babanmu ni da Yaya

Dijah da take tashe da tsohon cikinta in ban da

kuka babu abinda take yi, ni kam nayi kukan na

gaji na bari watakila don ban gama fahimta ba

ko gama gane girman abinda ya same ni shi yasa

na hakyra da kuka na koma zare ido.

To yaya za ayi ai sai hakuri kawai, ita kam ai

ta huta wajen haihuwa.ta rasu banda haka kowa

alherinta yake fada, dubi kuma irin mutanen da

ta samu, kiyi hakuri kawai ki bar kukan muyi ta

addu’a Ubangiji ya gafarta mata, muka ce

Amin.

Duk da hakurin da Babana ke ta bayarwa na

muyi hakuri sau biyu ina ganinshi ya buya a

dakinshi yana nashi kukan.

Rannan da safe Yaya Ibahim yazo gaishe mu

dama kuma tunda a ka watse zaman makokin bai

taba fashin zuwa gaisuwar ba, suna gama

gaisawa da Babana yayi tasa mishi albarka. Da

zai tafi kuwa sai ya ce mishi in ka taso daga

 

23

 

kasuwar ka biyo ta nan ka tafi da matarka taie

gida ta huta a dakinta, sai kayi ta hakuri da ita.

Ya ce, To Baba yayi mishi godiya ya tashi ya

tafi, rannan da yamma Yaya Dijah ta koma

dakinta ba a wani dade ba kuwa ta haihu, ya

mace ta haifa, Yaya Ibrahim ya sanya mata

sunan Innarmu daga mu har Babanmu muka yi

murnar alherin da yayi mana.

Babah Sumaye ce taje ta zauna mata tayi

mata biki har tayi arba’in saboda Yaya Ibrahim

da iyayenshi sun ki yarda da dawowanta gida

suka ce tunda babu, Inna to me za ta dawo gida

kuma tayi?

Sannu a hankali sai mutuwar Inna ta rinka

shigarmu tana ratsa tsoka da kashi da bargo da

zukatanmu, gaba daya ta makurkusa mu ta canza

mu daga yanayin da duk muke tun ma dai ba

Babana ba.

A farkon al’amarin ni kam ma gani na rinka

yi tamfar karya ne tana can asibitin. ne kawai

watarana zata dawo wani lokaci kuma in rinka

jin tanfar wani mummunan mafarki ne da zan

farka in ga al’amarin ya sauya in da duk abin ba

haka ba ne amma ina?

Sannu a hankali sai kwanakin suka fara tafiya

daga daya har a ka je uku a ka yi bakwai har aka

kwana arba’in ban ga Inna ta dawo ba, babu ita

 

24

 

 

babu dalilintà sai dai yan uwanta da abokan

arzikinta su dan zagayo su duba mu a duk sanda

za su tafi kuma hakuri ne dai suke ba mu tare da

fadin Ubangiji ya jikan Ramatu da rahamarsa, ya

kuma sa alherinta ya bita, amma ita kam shiru

kake ji.

Wannan shi ne abinda yafi komai ba ni tsoro,

a wannan lokacin sai na zama babu abinda nafi

so irin in zauna in yi ta kuka saboda na riga na

fidda ran sake ganinta tunda ban taba ganin

randa tayi tafiyar da ta wuni ta kwana ba tare da

ta tasa ni a gaba ta tafi dani ba.

In ban da kewarta da kadaicin babu abin da

yafi komai damuna, ko ina yayi min fadi gani

nake tanfar ni.kadai ce a raye babu wani abinda

nake ji in ji na gani su balle in ji dadinshi in

tsaya bayani, na kewar da Inna ta bar mu a ciki

ma to na 6ata bakina ne na kuma san duk yanda

nakai da jin wani abu’ kan rasata da aka yi to

Babana yafi ni, illa iyaka dai kawai shi baya

cewa komai.

In bani nayi mishi maganarta ba, ba ya yi

mini. In na cika kawo mishi zancenta ma sai ya

ce min yawaita yi mata addu’a zai fi yawaita

hirarta amfani in ce mishi to.

Tunda Inna ta rasu ba mu taba dora tukunya a

gidanmu da sunan yin girki ba, Babah Sumaye

25

 

ke sanya mana abinci rana da dare kamar yanda

ta rinka yi sanda Innarmu ke rashin lafiya.

Abin karyawa kuwa sayo mana nake yi wata

rana koko da kosai, wata rana waina da miya

wata rana shayi da burodi.

Kullum dai ni Babana yake tambaya me nake

so? In gaya mishi ya ce in je in da kudin suke in

dauko inje in saya, in na tati kan in dawo sai in

samu yayi sharar tsakar gida da kicin har da

wankin bayan gida muna gama karyawar sai in

tattara kwanukan da muka yi amfani da su in

wanke su in kife in uye ruwan wanka in je in yi.

Innata ma mata ce mai matukar tsabta, don

haka har bayan bata nan din ma ba ma iya barin

gidanmu da datti, kullum ka shigo tšab zaka

ganshi, kamshin turarenta ne dai a yanzu babu

shi a gidan.

Gidanmu gida ne na Jama, 8, kafin rasuwar

Inna amma a yanzu da bata nan wuni muke yi a

ciki babu wanda ya leko mu har yaran ma sun

daina zuwa dan gara gara ma Mansur jifa-jifa ya

kan shigo ya gaida Babana, ni kuma ya kawo

min dan wani abin lasawa.

Don haka nima ban cika zaman cikin gidan

ba in Jumare tana nan in shiga gidan Babah

Sumaye in bata nan in je wajen Babana in taya

shi sai da kayanshi sai ya taso in debo mishi

 

26

 

kwanduna mu dawo gida in shiga wurin Babah

Sumaye in karbo mana abincinmu mu zauna

muci tare a kwano daya ni da shi.

A duk ranar Juma’a kuma yakan sani in

shirya in je in gaida dangin Innata mafi yawanci

nafi zuwa gidan Yakunbo Halima wacce ita ce

yar Inna da take bi in naje wurinta wannan

Juma’ar sai wata Juma’ar, kuma in je wajen

Yaya Dijah.

Babana yana mutunta Yakunbo saboda sona

da take yi, sai dai duk da haka bai yarda ya bata

rikona ba duk da har turowa tayi a rokar mata

shi ya bata ni.

Sai ya ce a bata hakuri gani nan dai a tsakani

ai duk na ishe su. Tunda Yaya Dijah tayi arba’in

kusan duk sati sai tazo gidanmu sau biyu in zata

zo kuma takan zo mana da lafiyayyar miya

wacce take yi mana da naman kaji ko kayan

cikin saniya wata ran har ta kirbo mana sakwara

wai mijinta ne yake yin cefanen ya ce tayi ta

kawo mana mu rinka ajiyewa ko biredi ma rinka

ci da ita shima zuwanshi biyu wurin Babana kan

maganar ya basu ni.

Ya kalle shi yayi murmushi ya ce to in baku

ita Ibrahim kai da matarka ga kuma ‘yarku sai in

kara muku da ita ni fa? In zauna ni kadai? Ai ba

zan iya ba.

 

27

 

Surukuta mai dadi Babana yake yi da Ibrahim

da kawai ya maida shi saboda yayi sa’a shima

Ibrahim din mutumin kirki ne ga sanin darajar

surukuta.

Don haka Baba yana sonshi yana kuma son

diyarshi da ya yi wa Innarmu takwara da ita ba

kadan ba har ma sai yayi mata lakani yake

kiranta da suna.

Rannan ina jin Babana yana cewa Ibrahim

din ka gayawa Dijah ta daina zirga-zirga da

yarinyar nan a kan hanya tana diban mata sanyi,

ya dan yi murmushi cikin girmamawa ya ce, Ai

ba komai Baba, Babana ya ce a’a ta zauna aa

dakinta kawai zuwan nata ba wani dadi ne da shi

ba tunda maimakon tazo ayi wata magana da ita

sai tazo ta wuni tana kuka gara ta hakura kawai

ta zauna a dakinta ya ce to Baba, ya tashi ya tafi

tun daga nan sai ya zama kannenshi ne suka

kawo mana duk wani abin da za su aiko mana da

shi ita kuwa ta koma zuwa jifa-jifa.

Inna ta rasu ne cikin watan Jimadah Thani,

sannu a hankali sai gamu mun iso cikin watan

Sha’aban har shima ya kusa zuwa karshe mutane

sai shirye-shirye da dokin isowar Ramadan suke

yi mukam a gidanmu ba a shirin komai.

Da Inna tana nan da mu ma muna nan muna

ta shirye-shirye abinda zuciyata take ta gaya min

 

28

 

kenan sai dai ban gayawa Babana ba saboda

yawan ce min da yake yi mata addu’a yafi yawan

hirarta amfani.

Ana gobe za a fara Azumi Babana ya bani

sugar mudu bibbiyu da madarar (Peak) dozin

dai-dai ya sani na bi yayun Inna mata da ke

gidan aurensu na kaiwa kowacce nata na gidan

Babanta kuwa shi da kanshi yaje ya kai musu

haka nan gidan Baba Hodijo.

Yaya Dijah kuma mu ma ta aiko mana da

abubuwa masu yawa kala-kala kuma masu dadi

na kamun Azumi.

Washegari kuwa mai alfarma Sarkin Musulmni

ya bada sanarwar ganin watan Ramadana mai

albarka don daukacin Musulmi maza da mata

suka yi niyyar daukan Azumi.

Sanda Inna ke raye na kan yi Azumin amma

ba mai yawa ba, ban san dalili ba a wannan

lokacin sai Babana ya ki yarda sai da nayi tayi

mishi kuka ya bar ni na dauka har watan ya kai

ashirin kuwa ban yi abin da yafi guda bakwai ba.

Shiga goman karshe da aka yi ne ya nuna

gabatowar sallah karama daga ko’ina sai aiken

kayan sallah ake yi min dangin Inna maza da

mata zai wuya a ce ga wanda bai yi min ba, sai

dai kawai na wani yafi na wani haka kawayen

Inna da Iyayen ‘ya’yan da ta saba yi wa kitson

 

29

 

 

sallah da lalle kyauta, Babah Sumaye ma Yaya

Dijah da mijinta kam ba a maganarsu ga kuma

Yakunbo.

Babana ya tara kayan a gabanshi yana

dubawa, idanuwanshi suka cicciko da hawaye ya

ce, Wannan duk arzikin Ramatu ne Ubangiji ya

gafarta mata na ce mishi amin Baba.

Mun wayi gari a gidanmu ranar sallah kamar

yanda ta kasance a gidajen sauran Musulmi baki

daya, sai dai mu kam maimakon walwala da

farin ciki irin na sallah samun kanmu muka yi

cikin matsananciyar kewa.

Mutuwar Inna ta zamo mana sabuwa saboda

ganin babu kowa cikin kicin din gidanmu, da

yanzu tana nan tana fama da cincirindon yaran

dake karbar abincin sallah a kofar kicin dinta

wanda yawanci burabuskon gero take yi da

miyar yakuwa saboda shi ne mafi soyuwar abinci

a wurin Babana, sai kuma tayi masar shinkafa da

miya don rabo na sosai da sosai wanda ni zata yi

ta aika ina mikawa sai wadanda suka san da

burabuskon nata ne zaka ji suna aiko ni ki

gayawa Ramatu ta fa sanmun burabuskon nan

ina so, in ce musu to.

Yau kicin dinmu shiru babu kowa a cikinshi,

na shiga cikinshi har na gaji ina ganin kamar zan

 

30

 

ganta a mazauninta ban ganta ba, babu ita babu

dalilinta.

Ga fa kwanukan abinci nan an tara mana zo

ki zabar mana wanda zamu ci ki fitar da saura ki

samu masu ci ki basu don kar ya lalace nayi

maza na ce to Baba.

Nazo na dudduba na dauko kwanon

Yakunbo, tuwon shinkafa ne miyar kuka da man

shanu da yaji, ga kuma naman da nayi zaton na

Talo-Talo ne a ciki na ce mu ci wannan Baba ga

kuma masa da miya.

Mansur ya kawo na Yaya Dijah, kwan doya

ne da cincin mai nama da gasasshiyar kaza, sai

miya a wani kwano su na adana mana sauran

zan fitar in baiwa yaran da suke so ya ce, To.

Duk da lodin kayan sallar da ke gare ni ban

wani yi kwalliya ba,bayan wankan da nayi sai da

Babana ya ce min to gyara jikinki mana

Yahcuwuna kiyi kwalliya kamar sauran yara,

sannan naje nayi.

Nayi kyau ba kadan ba, ga kitsona da Babah

Sumaye tasa a ka yi min sun sauka har kafadata

na shiga gidan taga kwalliyata ta kuma aike ni

gidan su Jumare na kai musu abincin da tayi har

da gidan Yakunbo saboda mu’amallah sosai suke

yi a tsakaninsu.

 

31

 

 

Kwalliyar sallah sosai na rinka yi muka kuma

yi yawon sallah ni da Jumare wacce take ganin

ita din budurwa ce tunda ‘yanmata a wancan

lokacin sha hudu ne sha biyar in an yi tsanani

sha shida wacce ta makara sosai sha bakwai.

Har gidan zoo Jumare ta kai mu muka kuma

samu goron sallah, osai wurin dangi da kuma

masu son Jumare.

Tun sanda Innata ta rasu ban sake zuwa

Makarantar boko ba, ko kuma ta Alkur’ani, ina

zaune ne kawai a gida bana komai tanfar dai a ce

da gani har Babana nawa mancewa muka yi da

ana zuwa Makarantar sallah da sati guda.

Ina tare da Babana, labarin yawon sallarmu

da Jumare nake ba shi yana jinjina kai cikin

yanayi na nuna alamar murna da gamsuwa don

dai ya kara min jin dadi da na gama sai ya kalle

ni ya ce min, gobe kuma ina za ku ke nan?

Nayi dariya na ce babu, ai hidimar sallah ta

Kare tunda yau sallah na da kwana bakwai.

Ya sake kallona ai kuwa dai haka ne hidimar

sallah ta kare kenan, na ce eh Baba. Ya ce, To ai

ina ganin sai kiyi shiri ki soma zuwa

Makarantarki, kin ga kin dade ba ki je ba, in ma

kin ga ba za ki ta bokon ba shi ke nan amma ta

allo kam da ta Asuba sai ki rinka zuwa na sake

ce mishi to Baba.

 

32

 

 

Jimawa can ya sake kallona cikin natsuwa ni

a ta bokon aji nawa ki ke ne? a wancan lokacin

da ba a cika sanya yara a Makaranta kafin

cikarsu shekaru bakwai ba, saboda bin ka’idar

hannun dama ya taba kunnen hagu kafin a dauki

yaro a Makaranta sai na ce mishi aji uku.

Yayi maza’ya ce, A’a to ashe ma kin fara nisa

ina ganin har ita sai ki koma don ki samu ki

gama aji shidan ki koyi karatu da rubutu da dan

turancin kai yara asibiti.

Ban amsa ba saboda jin nauyi a dalilin gane

in da maganar tashi ta dosa, iyaka dai nayi shiru

don komawa kan karatuna da na bari nima yafi

min don zai rage min zaman kadaicin da nake

ciki.

Kwana biyu bayan nan na soma zuwa

Makarantar boko wanda sai da naje ta allo kafin

nayi hakan gab ake da fara jarrabawar canjin aji,

a lokacin da na koman sai, dai da yake dama can

ina cikin yaran ajin masų fahimta gashi kuma ina

da kawata da muke benci daya Hasiya Jibrin, sai

na samu hayewa zuwa aji hudu.

Rannan na dawo daga Makaranta na shiga

wajen Babah Sumaye karbar abincina na zauna a

nan wurinta ina ci muna hira tana bani labarin

al’amuran da take ganin ya kamata in sani, na

gama na mike na kai kwanon gun wanke-wanke

 

33

 

na hada da kwanukan da na samu a wurin na

wanke su tas, na kife na wuce bandaki nayi

wanka na fito na wanke uniform dna na shanya.

Na shiga dakinta na shafa mai na dauki

kayana da ke wurinta na fito ina rungume da

allona, na ce mata za ni Makaranta Babah, ta ce

a’a sai kin karbo min cefane, ajiye allon anan

kiyi gudu ki karbo min cefane ki kawo min sai ki

tafi, na ce mata to. Nayi yanda ta ce din kafin na

tafi makarantar.

 

Mu’amallah ta uwa da ‘yartga Babah Sumaye

take yi dani, yanda take tafiyar da ni sanda

Innata take raye haka a!’amarin yake, har yanzu

sai dai ma kari.

Don yanzu tana sa ido sosai a kaina hada

kayanki kiyi wanki, in ce to. Dauki kibiya ki

tsefe kanki, tunda ba wani son kits ake yi ba

in ce mata ban iya ba ta ce in gama abinda nake

yi in kawo kibiyata tayi min tsifan kowane

lokaci a cikin yi min fada take, sai dai in bata ga

nayi laifi ba ko da kuwa a gaban waye.

Ina ganin har dan hakanne yasa Yakunbo bata

dadewa bata zo wurinta ba, in tazo kuwa ta rinka

yi mata godiya ke nan, ita kuwa Yay. Dijah

kusan kullum in zata zo zata riko mata wani

abun hasafi ko dai sabulun wanka dana wanki ko

kayan tea.

 

34

A wannan lokacin a gida na daina barin

Babana yana sharar tsakar gida da kicin, ina idar

da sallah nake fita in yi komai in gama abin da

ke bukatar wanki in wanke na gyarawa in gyara

tunda ba wani kwanannen datti ba ne a gidan.

Sai kaga nan da nan nayi na gama na shiga

wankana, yawan abubuwan da Yaya Dijah kke

kawo mana kwana da yawan maganar da take yi

min kan fita kullum aje sayen abin karyawa

kowa yana gani yasa na rage sai in ce Baba muci

abu kazan da muke da shi kawai ya ce min to.

Kullum na gama shiri zan tafi Makaranta sai

Babana ya ce min matso nan in gyara miki hodar

nan taki, in ce to. In matsa yasa gefen rigarshi ya

goge min fuskata kafin ya umarce ni dasa hannu

in dauki Naira daya a cikin kudin da suke dakin,

lokacin nan kuwa Naiara daya ba karamin kudi

ba ne a wurin yara, don kuwa tana iya sayen

waina ta sayi biskit har ta hada da kwalbar lemo

wani lokaci ma har da alawa don haka kudi sosai

nake zuwa da su Makaranta.

Ina tare da Babana a gida duk da Innata ta

rasu yana matukar kula da ni, wai abin da yake

yi min din ma sanda Inna take nan bana samu,

don kuwa ita mai kwaba ce mai kulawa kuma da

tarbiya, iyaka dai kawai zama kusa da Inna da

 

35

 

yunwa yafi zama a inda bata nan cikin daula da

 

da na sha.

, Babana ya dawo daga Masallaci sallar asuba

ya zauna ya gama laziminshi da addu’ar da zai yi

ya gama ya shafa nima na shafa tunda a kusa da

Sinl nake zaune na soma gaishe shi kasancewar

ranar ta Lahadi ce ya sani gyara zama kusa dashi

tunda ba Makarantar boko zani ba.

Zan gama abin da zan yi ne in tafi makarantar

allo wannan kuwa sai wajen tara. Daga ido nayi

na kalli Babana cikin natsuwa na ce mishi Baba,

ya ce Na’ am Mamana, na tambaye shi yanzu duk

addu’o’in da muke yiwa Inna suna zuwa inda

take?

Yayi maza ya gyada kai tare da fadin da

yardar Ubangiji kuwa, kin san ai akwai wasa

ayyuka na sadakatul jariya masu gudana da dan

Adam kan bari a duniya ladar ta rinka kaiwa a

gare shi a bayan rayuwarshi daga cikin irin

wadannan ayyuka da ladansu bata yankewa

akwai ‘ya’ya na gari.

Ba kina sallolinki a kan kari ba? Nayi maza

na ce mishi eh babu, ba kya kuma sabon

Ubangiji da gangan, na girgiza kai nuna lamar

a’a, ya ce To in sha Allahu in kin yi addu’a ladan

zai kai gareta ga kuma Yayarki da take zaune a

dakin aurenta, tunda a ka yi aurenta ba’a taba jin

 

36

 

wani abu na rashin jin dadin game da ita ba, kin

gani? Cikin yardar Ubangiji addu’o’inku za su1

rinka kawai gare ta.

Na sake kallon shi a hankali na ce mishi

menene sabo Baba? Ya zuba min ido kafin ya

gano ta inda zai Bullowa lamarin, irin su karya,

gulma da shiga harkar da ba taka ba, da

bijirewa iyaye ko zina da makamantansu kin

gane?

Nayi maza na ce na gane, kusan kullum sai na

lissafawa kaina laifuffukan da Babana ya lissafa

min a matsayin zunubi ko sabo, don kar in aikata

su saboda kar in aikata su su zama sanadin da

addu’o’ina za su daina kaiwa ga Innata.

Kusan kullum na zauna tare da Babana muna

hira zai yi min nasiha da cewar in kasance mai

gaskiyaa kan al’amurana in kuma tsare

mutuncina kar in yarda wani yayi min wayo duk

abin da na gani naji ina so in gaya mishi ban da

karbar abin hannun wani ita mace bata da wata

daraja komai kyanta in har bata zama mai kamun

kal da tsare mutuncin rayüwarta ba, in ce mishi

to din ba tare da na san mé maganar tashi take

nufi ba har na gane komai.

Rannan na idar da sallar Asuba ina ta doki da

zumudin Babana ya shigo in ba shi labarin da ke

 

37

 

Cina a raina, yana shigowa na soma gaishe shi ba

tare da na jira ya kai mazauninshi.

Cikin natsuwa na kalle shi na ce mishi Baba

zan yi sadaka yau, ya kalle ni cikin natsuwa ya

ce sadakan me kike son yi uwata? Na ce ko na

meye ma Baba jiya da daddare nayi mafarkin

Inna wai tazo gidannan na ganta lullube da

fararen kaya tana kallona tana ta faman

murmushi ni kuma sai tambayarta nake yi Inna

dama ashe za ki iya zuwa wurinmu shi ne tunda

kika tafi baki taba zuwa kin duba mu ba, ni da

Babana?

Ina maganar tana kallona murimushinta kawai

take yi ni kuma ina kurarin matsawa kusa da ita

don in taba ta ina cewa Inna kiyi mini magana

mana har zan taba tan sai kawai naga ta 6ace sai

kuma kawai naga ra farka daga baccina.

Cikin natsuwa ya zuba min ido a allona

lokaci mai tsawo bai kawar da idamuwanshi daga

gare ni ba har na fara jin tsoro ko yayi fushi ne

saboda maganarta da nayi mishi tunda ya sha ce

min in an tunata ayi mata addu’a kawai basai an

yi zancenta wani ba har zan buda baki in bashi

hakuri tare da alkawarin ba zan sake yi mishi

hirarta ba sai naji ya ce min jiyan da kika yi

mafarkinta ai jiyan ta shekara.

 

38

 

Nayi maza na daga ido na kalle shi a firgice

saboda razanar da nayi sai ya ce min kin gani in

ha ki manta ba ta rasu ne ranar sha tara ga waran

Jimada Thani, to yau ma ai shataran ne ko

ashirin ga watan.

Na ce Haka ne Baba, lokaci mai tsawo ya

dauka yana yi mata addu’a tare da sauran

Jama’ar Musulmi da suka rigaye mu baki daya

in kuma tamu cikawar tazo to Ubangiji ya

azurtamu cikawa da kyau da Imani.

Nayi maza na ce amin Baba tsawon lokaci

muna zaune shiru babu wanda ya sake furta wata

magana sai na bude baki da nufin fadin abinda

ke kai kawo cikin raina a hankali na soma yin

maganar cikin yanayin girmamawa da tsoro don

kar ya hana ni abin da nake nufin fadin tunda

yasha gaya min cewar maimakon yawan

ambaton Inna da yawan maganarta mu rinka

yawan yi mata addu’a kawai.

Zuba min idon da yayi yana kallona shi ne ya

kara tabbatar min da cewar ni yake sauraro, don

haka cikin natsuwa da ladabi sai na buda baki

nace mishi Baba tafiyar ta Inna ta fara nisa duk

da a lissafi ne kawai Inna ke da shekara guda a

yanzu in a kewa da kadaicinta ne mun kai wani

matsayi da ba zai yiwu mu kwatanta ba.

 

 

39

 

Duk da haka shekara gudan lisafin ma lokaci

ne mai tsawo da yawa in ban da tafiyar tata bata

dawowa ba ce da yanzu ta dawo ko kuma damun

soma sa rai da dawowan nata.

Cikin natsuwa ya ce min eh, Maryam ai tafiya

taia wata irin tafiya ce da dadewa bai sawa a

dawo da dadewa kansa a dawo ai da mu ma

iyayenmu sun dade da dawowa.

Nayi maza na ce haka ne Baba, kamar in yi

mishi wata maganar sai kuma naga to bari kawai

in ja bakina in yi shiru.

Kamar in sake yin wata maganar sa kawai

naga bari kawai in ja bakına in yi shiru.

A wannan lokacinne na shiga aji shida na

Makarantar Primary na fara girmia har Babana ya

fara barina ina tafiya gidan Yayc Dijah ni kadai

don yi mata wuni. Ina matukar son awa gidanta

saboda yanda na lura na gane bata da wani

wanda take so da kyautatawa irina.

Kullum naje gidanta to bata gajiya da tattalina

da tarairayata komai na ce mai kyau ne cewa

take yi in dauka tana ganin na kwana biyu ban je

ba zata shiga aiko kanen mijinta suzo su ga

lafiyata, in kuwa naje bayan aiken nata zan

gamu da fushinta kan dadewan da nayi ban je ba

kullum a cikin yi min nasiha take tana ganin zani

aikata kuskure zata yi maza ta gyara min.

 

40

 

 

Yanda Yaya Dijah ke sona da ji da ni haka

shima mijinta yana ganina zai fara murmushi ina

Inna take? Zo maza ga Mamanki tazo.

Sanin da yayi kullum naje gidan Yaya Dijah

zata tasa ni a gaba da aikace-aikace har da su

hidimar girki wai kar in girma ban iya aikin

mace a gidanta ba, yasa yana ganina zai je yayi

sabon cefane ya kawo ko da kuwa ba a ranar

suke bukatar cefanen ba sai ya ce in na girka in

tafi mana dashi gida muyi amfani da shi ni da

Baba.

Ina son Yaya Dijah da mijinta ina kuma

matukar son ‘ya’yanta Inna da Abbati, ina son su

irin son da ba zai kwatantu ba, saboda gani nake

tamfar su din su kadai sune dangin da nake da su

sai kuma nake kallonta kallo irin na uwa, ganinta

nake tamfar ita ce madadin Innata da na rasa.

Dangin mijinta kuma ‘yan uwa saboda suna

sonta kowane lokaci kaje’gian sunanan aurenta

aure ne na soyayya, fahimta da kuma kyautatawwa

juna, don haka gidanta gida ne na farin ciki da

kwanciyar hankali, kudi masu yawa ne kawai ba

su da su amma suna cikin rufin asiri.

Ni da Yaya Dijah kamannin da ke tsakaninmu

ba wasu masu yawa ba ne, ba su wuce wadanda

zaman ciki na kasancewa shakikai ke haddasawa

 

41

 

ba, yayin da nake matukar kama da Innarmu ita

kuma kama da Babanmu take yi.

Haka nan ko a halayenmu mun bambanta

mace ce mai matukar hakuri bata kuma da

kwaramniya.

A wannan lokacin saboda na riga na fara yin

wayo na fara fahimtar me nake ciki sai na zama

babu abin da nake so nake fata da buri irin in

ganni nayi haddar Alkur’ani mai girma a dalilin

kullum sai Malaminmu na Alkur’ani yayi mana

bayani kan falala, girma da kuma darajar

mahaddata Alkur’ani a ranar alkiyama su da

yayensu.

Sai na zamo ina matukar kwadayin nima

iyayena musamman ma Innata da nake rayuwa

cikin tsananin kewarta da begenta su samu irin

wannan matsayin a gobe kiyama.

Kowane lokaci a cikin taka tsan-tsan nake na

kauce wa aikata laifi musamman yin karya da

duk wani abin da Mallaminmu ya ambata cewwar

laifi ne don in samu in zama ya ta kwarai

saboda ya ce mana ya’ya na kwarai suna daga

cikin sadakatul jariya da mutum ke bari a duniya

wanda ladansu ba su yankewa a gare shi.

Rannan ina tare da Babana a cikin gidanmu

da daddare a kishingide yake a kan tabarma

yayin da yake jan carbinshi a hankali cikin

 

42

 

natsuwa idanuwanshi a kaina suke tare da

natsuwar shi saboda sauraron haddar da nake

kawowa na suratul ‘ANKABUT”.

Sai da na kai karshe na sake kallonshi cikin

natsuwa kan in gaya mishi abinda nake nufin

gaya mishin sai ya ce min kina da murya ta

karatun Alkur’ani Maryamu, kar ki yarda ki

daina, kar ki yarda kiyi wasa ta basirarki na ce

mishi to Baba, kan in yi wata magana sai ya sake

bani umarmi na in maimaita surar, ya ji ta dá

kyau.

Sau biyu na maimaita sannan yayi murmushi

ya ce a’a lalle hadda ta zauna sai kiyi ta tilawa

kar ki yarda kina yin sake don shi Alkur’ani

kana barinshi sai shima yayi nesa da kai, don

haka ki dage da tilawarshi. nayi maza na ce to

Baba. Yi mana addu’a, na sake cewa to nayi

muka shafa sannan muka je muka kwanta.

Rannan da safe muna aikace-aikacenmu a

gida ni da Babana kafin ya fita kasuwarshi nima

in tafi Islamiyyata tunda ranar ta Asabar sai naji

ya ce min ni Mero ba ki iya komai ba ne cikin

girke-girken da ki ke cewa ‘yar uwarki tana nuna

miki?

Nayi maza na bar abinda nake yi na kalle shi

Cikin natsuwa da zumudi na ce mişhi Baba duk

abincin da nake zuwa da shi gidan nan fa ni nake

43

 

yi Yaya Dijah zama kawai take yi tana kallo in

taga zan yi wani abu ba daidai ba ta gyara min.

Shiru yayi yana kallon wuri guda nuna alamar

a cikin tunani yake, na bar abinda nake yi na

sake kallonshi tare da tambayarshi mene ya

faru Baba? Kaji miyar bata yi dadi ba ne?

Yayi maza ya gyada kai uh’uh ba haka ba ne

Mero tunani dai nake yi na in har ke ce da gaske

ki ke yiwo mana wannan girkin to ai gara in

hutar da wadannan yan uwa namu da suke ta

faman dawainiya damu shekara guda har da

wasu watanni tunda mahaifiyarku ta rasu ba su

taba hutawa da hidimarmu ba.

Don haka in har za ki iya to sai in sauke musu

nauyin girkinmu su rinka.yin nasa kawai in rinka

kawo cefanenmu kina yi mana.

Nayi maza na ce eh Baba gara kawai muyi

hakan can cikin zuciyata murna nake yi da

zumudi saboda babu abin da nake so nake kuma

sha’awa irin in ganni ina girki ni kadai ba tare da

ana nuna min ba wai ni a dole na iya.

Wannan maganar da muka yi da Babana bata

wani dade ba don ko kwana bakwai bata yi ba,

naje karbo cefane kamar kullum yanda na saba

ni ke zuwa wurin shi in karbo cefanen kayan

miya gami da su manja ko man gyada da maggi

 

44

in kai ma Babah Sumaye shikuma Baba Hodijo

yayi abin da ya saura tare da hatsi.

Ina tsaye ina jiran ta gama hada min in dauka

in kawo mata sai kawai naga ya miko min ledoji

guda biyu, ungo ki kai mata daya ke kuma ki

girka mana daya.

Gabana ya yanke ya fadi tamfar dai’ ba ni ce

na ce mishi na iya girkin ba. Zaro idanuwa nayi

ina kallonshi yayin da shi kuma ya ci gaba da yi

min bayani, na riga na yi wa Mallam Hodijo

bayanin komai, don haka kaiwa ita uwar taki

kunshi daya ki rike daya.

Kije ki girka mana abinda ki ka san shi ki ka

fi iyawa kin gane ko? Na ce mishi to Baba, na

kamo hanya ina dawowa gabana sai faduwa yake

yi ban taba yin girki ni kadai babu wani babba a

wuri ba hasalima kafin rasuwar Innata bana

shiga kicin da sunan ya yi girki ko da kuwa na

wasa ne.

Babah Sumaye ta zubawa cefanen ido tana

kallo yanzu nan bawan Allahn nan da gaske yake

yi sai ya raba girkin nan? Ta dan gyada kai tare

da fadin to ai shi kenan tunda haka ya gani

daya,

amma menene’? Ai mun riga mun zama

dan abincin da a ke sa mishi guda nawa yake?

Ban da haka ma kullumn fa cefanen nan a

wurinshi ake karbo shi amma ya ce wai

 

45

dawainiyar da ake yin tayi yawa, ni dai nafi

zaton ko subutan bakin da nayi na ce a gaya

mishi ga wata bazawara na saman mishi ne duk

ya kawo hakan.

Ni kuma ba nayi hakan ne don na gaji a sa

mishi tuwo ba a’a ko kadan ba haka ba ne nayi

mishi tallan bazawarar ne don ganin hankalinta

da natsuwarta shi kuma yana ta zaune a haka yau

kusan shekara daya da rabi da rasuwar Ramatu,

wanda wasu da kyar suke jira ayi arba’in sai

kawai ka ji sun daura aurensu.

Yanda dama ban san anyi wannan magana da

Babah Sumaye ta rattaba min ba haka a yanzun

ma da ta rattaba min ban nuna naji ko na gane

inda Zancen nata ya nufa ba, balle in furta wata

kalma.

Sa hannu kawai nayi na dauki leda guda daya

na juyå da nufin fita daga gidan saboda nima ban

san dalili ba sai naji maganar ta dan sosa min

zuciya ina fita daga gidan dai ina jinta tana cewa

bai fahimce ni ba ne, ban gaya mishi hakan don

ban damu da rashin da aka yi ba sai dai don

sanin da nayi cewar yanda duk muka kai da son

Ramatu to babu yanda za muyi tunda ta riga tayi

tafiyar da babu dawowa a cikinta sai dai kawai

muyi ta binta da addu’a.

About the author

Hausa_Novels

1 Comment

Leave a Comment