Bita Da Kulli Hausa Novel Complete
*BITA DA KULLI*
*NA*
*HASSANA Y.IYAYI*
*MAMAN NOOR*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER’S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
”'{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}”’
**
1
Misalin karfe 6:30 na safiyar litinin ya gama shirin tafiya kasuwa kasancewarsa irin mutanan nan abota sammako wani lokacin ma acan yake samun koko da kosai yayi kalacin safe. Har ya kai tsakiyar zauren nan yayi tozali da katon kwalli an dan bude bakinsa kadan, mamaki ya cika shi, tun yaushe kwallin yake a gurin, iya saninsa lokacin da ya fita sallar asubahi bai ga komai ba, cikin mutuwar jiki hadi da tsoro wanda lokaci guda sukayi masa dirar mikiya yake ayyanwa a rainsa kar dai wani mugun abun aka kunso aka ajiye masa a hankali ya motsa bakinsa da miyan bakin ya kafe tsoronsa Allah tsoronsa *bita da kullin*
mutanan unguwar a hankali ya furta.
The virgin maid Hausa Novel Complete
” Innallilahi ! me idona yake gani na shiga uku ” kirjinsa yayi nauyi hadi da wani irin lugude tamkar an daka da tabare da hanzari ya karasa gurin babu inda baya rawa a jikinsa tsoro mai tsanani ya kama shi tamkar ya bude kwalli nan yayi ta maza ya ja da baya murja ido yayi hadi da karasawa gaban kwallin,babu ko tantama biyo shi akayi bayan ya dawo salla aka ajiye bai rufe kofar ba saya kofar yayi ya wuce ka sa kunne yayi, ai kuwa ya fara jin kukan jariri na tashi kasa_kasa ga dukan alamu ya dade ya na kukan har muryansa ta dan dakushe dafe kirjinsa yayi tamkar kafarsa bazata iya daukarsa ba ya jingina da bangon zaure yana fadin.
” Na shiga uku na lalace ni Mansur me zan gani da asubahin nan jariri wallahi jariri ne kai jama’a” dan matsawa yayi a rude kusa da inda kwalli yake nan a ya she, ya kara bude idon dan dai ya tabbatar ba gizo idonsa ke yi ba cikin hanzari hadi jan kafa ya koma baya, cike da tashin hankali ko ganin gabansa ba yayi ya kada baki ya shiga kiran Ramma dake kwarya daki kwance tana bacci kira
“Ramma!Ramma yi da jiki dan Allah ki tashi daga wannan baccin asarar da ya zame miki jiki, da jijjiya ki fito masifa ta same mu zo ki ta ya ni gani masifa da asubahin fari fito mana Ramma ”
A sukwane Rahmatu ta fito ta saki hamma hadi da murza ido ga dukan alamu baccin bai isheta ba dan ga yawun bacci nan da shatti tabarma rudu -rudu a gefen fuskarta, cikin muryan wanda ya tashi a bacci take fadin.
“Allah ya raba mu da masifa malam me ya faru ne duk ka rude haka yi min bayani da manyan baki in tsaka da mafarkin an kawo min zakkar yan dubu -dubu ka ka tse min wannan daddan bacci”
Cikin sarkewar murya hadi da inda-inda ya fara magana
” Dan Allah kiyi min shiru ana ga yaki kina ga kura ba ki da zance sai na maganar da bata da amfani kudi dai kudai kamar kiyi sata mu je zaure ki gani lallai mutanan unguwar nan har yanzu sunan da mugun nufin su akan mu basu daina bin mu da Bita da kulli ba …” kafin ya kai ga rufe baki kukan jaririn har tsakar gidan dafe kirji Ramma tayi ta kankace ido ta ce
” A’a dakata min kamar kukan jariri kune na ke jiyo min ko dai jin kunne ne? ya illahi malam! ‘yar wa ka haikewa ni Ramma! wannan abi kunya da yawa yake na banu na lalace ” cike da tsoro hadi da far gaba Malam Mansur ya ce
“Shiga hankalinki ma na haba Ramma ! ni kike jifa da wannan mummunar kalmar, wallahi tallahi kin ji rantsuwar dan musulumi yanzu nan fitar da zanyi na ci karo da kwallin kar ki sa jama’a su dauka da gaske ne kiyi kasa da murya dan Allah “. Takamar wanda aka tankada a haukace tayi zauren daurin zani na ballewa jikinta har tsuma yake.
Hannu na rawa ta bude kwallin yayin da idon ya fada kan jaririyar da ke kwance tana canyara kuka yarinya kyakyawar gaske an shiryata cikin tsadaddun kayan jarirai masu taushi kasa dauke ido ta yi daga kanta lokaci guda kaunar jaririyar ta tsirga mata har rainta.
Cikin kidima ta dora hannu aka ta shiga kururuwa.
“Wayyo Allah mun bani mun lala ce! ke duniya ina zaki damu dauki jama’a an ajiye ma na jaririya a tsaure wannan masifa har ina wacce bakar dagar ce ta haife cikin shege ta zo ta ajiye mana a soro ”
Kafin ka ce meye wannan kofar gidan Malam Mansur ya dinke da jama’a tuni masu recording suka shiga dauka ana salati dan yanzu kiris ake jira a samu na watsa a social media
” Duniya ina zaki da mu tubarkallah! ku kalli jaririyar nan jawur da ita san kuwa kin wanda ya rasa yanzu uwar ‘yar nan bata ji kunyar goyon cikin ba, sai kunyar raino kai wannan rayuwa Allah ya saka miki duniya gidan banza inda ranka ka sha kallo muna jin wai-wai a gari ga shi ya ishe mu har cikin unguwa”
Mutane kowa sai tofa albarkar cin bakinsa yake nan masu watsawa a media kuma suka shiga yadawa harda karin kanzan kurege wasu ma cewa suke a buhu aka kulle jaririya ko yanke mata cibi ba’ayi ba kamar jira ake mutane suka shiga ruwan comments.
“Yanzu dai gidan mai unguwa ya kamata mu fara kai yarinyar nan sannan mu wuce gurin yan sanda ko? “Malam Mansur ya fada yana dauke kwallin da aka sanya jaririyar a ciki kallon kasan kwalli yayi nan idonsa ya fada kan wata farar takarda dake shinfide a kasan kwallin …….
[…] Bita Da Kulli Hausa Novel Complete […]
[…] Bita Da Kulli Hausa Novel Complete […]